< Isaiah 13 >

1 The burden of Babel, which Isaiah the sonne of Amoz did see.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Lift vp a standard vpon the hie mountaine: lift vp the voyce vnto them: wagge the hand, that they may goe into the gates of the nobles.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 I haue commanded them, that I haue sanctified: and I haue called ye mightie to my wrath, and them that reioyce in my glorie.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 The noyse of a multitude is in the mountaines, like a great people: a tumultuous voyce of the kingdomes of the nations gathered together: the Lord of hostes nombreth the hoste of the battell.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 They come from a farre countrey, from the end of the heauen: euen the Lord with the weapons of his wrath to destroy the whole land.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Howle you, for the day of the Lord is at hande: it shall come as a destroier from the Almightie.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 Therefore shall all hands be weakened, and all mens hearts shall melt,
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 And they shalbe afraid: anguish and sorowe shall take them, and they shall haue paine, as a woman that trauaileth: euery one shall be amased at his neighbour, and their faces shalbe like flames of fire.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Beholde, the day of the Lord commeth, cruel, with wrath and fierce anger to lay the land wast: and he shall destroy the sinners out of it.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 For the starres of heauen and the planets thereof shall not giue their light: the sunne shalbe darkened in his going foorth, and the moone shall not cause her light to shine.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 And I will visite the wickednes vpon the worlde, and their iniquitie vpon the wicked, and I wil cause the arrogancie of the proud to cease, and will cast downe the pride of tyrants.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 I will make a man more precious then fine golde, euen a man aboue the wedge of golde of Ophir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 Therefore I will shake the heauen, and the earth shall remooue out of her place in the wrath of the Lord of hostes, and in the day of his fierce anger.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 And it shall be as a chased doe, and as a sheepe that no man taketh vp. euery man shall turne to his owne people, and flee eche one to his owne lande.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Euery one that is founde, shall be striken through: and whosoeuer ioyneth himselfe, shall fal by the sworde.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Their children also shall be broken in pieces before their eyes: their houses shall be spoiled, and their wiues rauished.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Beholde, I will stirre vp the Medes against them, which shall not regarde siluer, nor be desirous of golde.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 With bowes also shall they destroy ye children, and shall haue no compassion vpon the fruit of the wombe, and their eies shall not spare the children.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 And Babel the glorie of kingdomes, the beautie and pride of the Chaldeans, shall be as the destruction of God in Sodom and Gomorah.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 It shall not bee inhabited for euer, neither shall it be dwelled in from generation to generation: neither shall the Arabian pitch his tents there, neither shall the shepheardes make their foldes there.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 But Ziim shall lodge there, and their houses shall be ful of Ohim: Ostriches shall dwel there, and the Satyrs shall dance there.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 And Iim shall crie in their palaces, and dragons in their pleasant palaces: and the time thereof is readie to come, and the daies thereof shall not be prolonged.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaiah 13 >