< Genesis 37 >

1 Iaakob nowe dwelt in the lande, wherein his father was a stranger, in the lande of Canaan.
Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
2 These are the generations of Iaakob, when Ioseph was seuenteene yeere olde: he kept sheepe with his brethren, and the childe was with the sonnes of Bilhah, and with the sonnes of Zilpah, his fathers wiues. And Ioseph brought vnto their father their euill saying.
Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
3 Nowe Israel loued Ioseph more then all his sonnes, because he begate him in his old age, and he made him a coat of many colours.
Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
4 So when his brethren sawe that their father loued him more then all his brethren, then they hated him, and could not speake peaceably vnto him.
Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
5 And Ioseph dreamed a dreame, and told his brethren, who hated him so much the more.
Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
6 For he saide vnto them, Heare, I pray you, this dreame which I haue dreamed.
Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7 Beholde nowe, wee were binding sheues in the middes of the field: and loe, my shefe arose and also stoode vpright, and behold, your sheues compassed rounde about, and did reuerence to my shefe.
Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
8 Then his brethren saide to him, What, shalt thou reigne ouer vs, and rule vs? or shalt thou haue altogether dominion ouer vs? And they hated him so much the more, for his dreames, and for his wordes.
Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
9 Againe hee dreamed an other dreame, and tolde it his brethren, and saide, Behold, I haue had one dreame more, and beholde, the Sunne and the Moone and eleuen starres did reuerence to me.
Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
10 Then he tolde it vnto his father and to his brethren, and his father rebuked him, and saide vnto him, What is this dreame, which thou hast dreamed? shall I, and thy mother, and thy brethren come in deede and fall on the ground before thee?
Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
11 And his brethren enuied him, but his father noted the saying.
’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
12 Then his brethren went to keepe their fathers sheepe in Shechem.
To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
13 And Israel said vnto Ioseph, Doe not thy brethren keepe in Shechem? come and I will send thee to them.
Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
14 And he answered him, I am here. Then he saide vnto him, Goe now, see whether it bee well with thy brethren, and how the flocks prosper, and bring me word againe. so hee sent him from the vale of Hebron, and he came to Shechem.
Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
15 Then a man found him: for lo, hee was wandring in the fielde, and the man asked him, saying, What seekest thou?
sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
16 And he answered, I seeke my brethren: tell me, I pray thee, where they keepe sheepe.
Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
17 And the man said, they are departed hece: for I heard them say, Let vs goe vnto Dothan. Then went Ioseph after his brethren, and found them in Dothan.
Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
18 And when they sawe him a farre off, euen before he came at them, they conspired against him for to slay him.
Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
19 For they sayd one to another, Behold, this dreamer commeth.
Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
20 Come now therefore, and let vs slay him, and cast him into some pitte, and wee will say, A wicked beast hath deuoured him: then wee shall see, what will come of his dreames.
Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
21 But when Reuben heard that, he deliuered him out of their handes, and saide, Let vs not kill him.
Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
22 Also Reuben saide vnto them, Shed not blood, but cast him into this pitte that is in the wildernesse, and lay no hande vpon him. Thus he said, that he might deliuer him out of their hand, and restore him to his father againe.
Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
23 Now when Ioseph was come vnto his brethren, they stript Ioseph out of his coate, his particoloured coate that was vpon him.
Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
24 And they tooke him, and cast him into a pit, and the pit was emptie, without water in it.
suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
25 Then they sate them downe to eate bread: and they lift vp their eyes and looked, and behold, there came a companie of Ishmeelites from Gilead, and their camels laden with spicerie, and balme, and myrrhe, and were going to cary it downe into Egypt.
Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
26 Then Iudah said vnto his brethren, What auaileth it, if we slay our brother, though wee keepe his blood secret?
Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
27 Come and let vs sell him to the Ishmeelites, and let not our handes be vpon him: for he is our brother and our flesh: and his brethren obeyed.
Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
28 Then the Midianites marchant men passed by, and they drewe foorth, and lift Ioseph out of the pit, and solde Ioseph vnto the Ishmeelites for twentie pieces of siluer: who brought Ioseph into Egypt.
Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
29 Afterwarde Reuben returned to the pit, and beholde, Ioseph was not in the pit: then he rent his clothes,
Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
30 And returned to his brethren, and said, The childe is not yonder, and I, whither shall I goe?
Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
31 And they tooke Iosephs coate, and killed a kidde of the goates, and dipped the coate in the blood.
Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
32 So they sent that particoloured coat, and they brought it vnto their father, and saide, This haue we founde: see nowe, whether it be thy sonnes coate, or no.
Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
33 Then he knewe it and said, It is my sonnes coate: a wicked beast hath deuoured him: Ioseph is surely torne in pieces.
Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
34 And Iaakob rent his clothes, and put sackecloth about his loynes, and sorowed for his sonne a long season.
Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
35 Then all his sonnes and all his daughters rose vp to comfort him, but he woulde not be comforted, but said, Surely I will go downe into the graue vnto my sonne mourning: so his father wept for him. (Sheol h7585)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
36 And the Midianites solde him into Egypt vnto Potiphar an Eunuche of Pharaohs, and his chiefe stewarde.
Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.

< Genesis 37 >