< Genesis 21 >

1 Nowe the Lord visited Sarah, as he had saide, and did vnto her according as he had promised.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 For Sarah conceiued, and bare Abraham a sonne in his olde age, at the same season that God tolde him.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 And Abraham called his sonnes name that was borne vnto him, which Sarah bare him, Izhak.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 Then Abraham circumcised Izhak his sonne, when he was eight dayes olde, as God had commanded him.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 So Abraham was an hundreth yeere olde, when his sonne Izhak was borne vnto him.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 Then Sarah said, God hath made me to reioyce: all that heare will reioyce with me.
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 Againe she said, Who would haue saide to Abraham, that Sarah shoulde haue giuen children sucke? for I haue borne him a sonne in his olde age.
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 Then the childe grewe and was weaned: and Abraham made a great feast the same day that Izhak was weaned.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 And Sarah sawe the sonne of Hagar the Egyptian (which she had borne vnto Abraham) mocking.
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 Wherefore she saide vnto Abraham, Cast out this bond woman and her sonne: for ye sonne of this bonde woman shall not be heire with my sonne Izhak.
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 And this thing was very grieuous in Abrahams sight, because of his sonne.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 But God said vnto Abraham, Let it not be grieuous in thy sight for the childe, and for thy bonde woman: in all that Sarah shall say vnto thee, heare her voyce: for in Izhak shall thy seede be called.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 As for the sonne of the bond woman, I will make him a nation also, because he is thy seede.
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 So Abraham arose vp early in ye morning, and tooke bread, and a bottell of water, and gaue it vnto Hagar, putting it on her shoulder, and the childe also, and sent her away: who departing wandred in the wildernesse of Beer-sheba.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 And when the water of the bottell was spent, she cast the childe vnder a certaine tree.
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 Then she went and sate her ouer against him a farre off about a bowe shoote: for she said, I will not see the death of the child. and she sate downe ouer against him, and lift vp her voyce and wept.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 Then God heard the voyce of ye childe, and the Angel of God called to Hagar from heauen, and said vnto her, What aileth thee, Hagar? feare not, for God hath heard the voyce of the childe where he is.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Arise, take vp the childe, and holde him in thine hand: for I will make of him a great people.
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 And God opened her eyes, and she sawe a well of water. so she went and filled the bottell with water, and gaue the boy drinke.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 So God was with the childe, and he grewe and dwelt in the wildernesse, and was an archer.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 And he dwelt in the wildernesse of Paran, and his mother tooke him a wife out of the land of Egypt.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 And at that same time Abimelech and Phichol his chief captaine spake vnto Abraham, saying, God is with thee in all that thou doest.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Nowe therefore sweare vnto me here by God, that thou wilt not hurt me, nor my children, nor my childrens children: thou shalt deale with me, and with the countrey, where thou hast bene a stranger, according vnto the kindnesse that I haue shewed thee.
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 Then Abraham said, I will sweare.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 And Abraham rebuked Abimelech for a well of water, which Abimelechs seruants had violently taken away.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 And Abimelech saide, I knowe not who hath done this thing: also thou toldest me not, neither heard I of it but this day.
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 Then Abraham tooke sheepe and beeues, and gaue them vnto Abimelech: and they two made a couenant.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 And Abraham set seuen lambes of the flocke by themselues.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 Then Abimelech said vnto Abraham, What meane these seuen lambes, which thou hast set by themselues?
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 And he answered, Because thou shalt receiue of mine hand these seuen lambes, that it may be a witnes vnto me, that I haue digged this well.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Wherefore the place is called Beer-sheba, because there they both sware.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 Thus made they a couenant at Beer-sheba: afterward Abimelech and Phichol his chiefe captaine rose vp, and turned againe vnto the land of the Philistims.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 And Abraham planted a groue in Beer-sheba, and called there on the Name of ye Lord, the euerlasting God.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 And Abraham was a stranger in the Philistims land a long season.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.

< Genesis 21 >