< Genesis 10 >

1 Now these are the generations of the sonnes of Noah, Shem, Ham and Iapheth: vnto whom sonnes were borne after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 The sonnes of Iapheth were Gomer and Magog, and Madai, and Iauan, and Tubal, and Meshech, and Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 And the sonnes of Gomer, Ashkenaz, and Riphath, and Togarmah.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Also the sonnes of Iauan, Elishah and Tarshish, Kittim, and Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 Of these were the yles of the Gentiles deuided in their landes, euery man after his tongue, and after their families in their nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Moreouer, ye sonnes of Ham were Cush, and Mizraim, and Put, and Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 And the sonnes of Cush, Seba and Hauilah, and Sabtah, and Raamah, and Sabtecha: also the sonnes of Raamah were Sheba and Dedan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 And Cush begate Nimrod, who began to be mightie in the earth.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 He was a mightie hunter before the Lord. wherefore it is saide, As Nimrod the mightie hunter before the Lord.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 And the beginning of his kingdome was Babel, and Erech, and Accad, and Calneh, in the land of Shinar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 Out of that land came Asshur, and builded Niniueh, and the citie Rehoboth, and Calah:
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Resen also betweene Niniueh and Calah: this is a great citie.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 And Mizraim begate Ludim, and Anamim, and Lehabim, and Naphtuhim.
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Pathrusim also, and Casluhim (out of whom came the Philistims) and Caphtorims.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Also Canaan begat Zidon his first borne, and Heth,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 And Iebusi, and Emori, and Girgashi,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 And Hiui, and Arki, and Sini,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 And Aruadi, and Zemari, and Hamathi: and afterwarde were the families of the Canaanites spred abroade.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 Then the border of the Canaanites was from Zidon, as thou commest to Gerar vntil Azzah, and as thou goest vnto Sodom, and Gomorah, and Admah, and Zeboijm, euen vnto Lasha.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 These are the sonnes of Ham according to their families, according to their tongues in their countries and in their nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Vnto Shem also the father of all the sonnes of Eber, and elder brother of Iapheth were children borne.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 The sonnes of Shem were Elam and Asshur, and Arpachshad, and Lud, and Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 And the sonnes of Aram, Vz and Hul, and Gether and Mash.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Also Arpachshad begate Shelah, and Shelah begate Eber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Vnto Eber also were borne two sonnes: the name of the one was Peleg: for in his dayes was the earth diuided: and his brothers name was Ioktan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Then Ioktan begate Almodad and Sheleph, and Hazarmaueth, and Ierah,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 And Hadoram, and Vzal, and Dicklah,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 And Obal, and Abimael, and Sheba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 And Ophir, and Hauilah, and Iobab: all these were the sonnes of Ioktan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 And their dwelling was from Mesha, as thou goest vnto Sephar a mount of the East.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 These are the sonnes of Shem according to their families, according to their tongues, in their countreis and nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 These are the families of the sonnes of Noah, after their generations among their people: and out of these were the nations diuided in the earth after the flood.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genesis 10 >