< Genesis 20 >

1 Afterward Abraham departed thence toward the South countrey and dwelled betweene Cadesh and Shur, and soiourned in Gerar.
Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi wajajen Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. Ya zauna a Gerar na ɗan lokaci,
2 And Abraham said of Sarah his wife, She is my sister. Then Abimelech King of Gerar sent and tooke Sarah.
a can ne Ibrahim ya ce game da matarsa Saratu, “Ita’yar’uwata ce.” Sai Abimelek sarkin Gerar ya aiko a kawo masa Saratu.
3 But God came to Abimelech in a dreame by night, and said to him, Beholde, thou art but dead, because of the woman, which thou hast taken: for she is a mans wife.
Amma wata rana da dad dare Allah ya zo wa Abimelek a cikin mafarki ya ce masa, “Kai da matacce ɗaya kuke, saboda matar da ka ɗauka. Ita matar aure ce.”
4 (Notwithstanding Abimelech had not yet come neere her) And he said, Lord, wilt thou slay euen the righteous nation?
Abimelek dai bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ya Ubangiji za ka hallaka al’umma marar laifi?
5 Said not he vnto me, She is my sister? yea, and she her selfe said, He is my brother: with an vpright minde, and innocent handes haue I done this.
Ba shi ne ya ce mini, ‘Ita’yar’uwata ba ce,’ ita ma ba tă ce, ‘Shi ɗan’uwana ba ne’? Na yi haka da kyakkyawan nufi da hannuwa masu tsabta.”
6 And God saide vnto him by a dreame, I knowe that thou diddest this euen with an vpright minde, and I kept thee also that thou shouldest not sinne against me: therefore suffered I thee not to touche her.
Sai Allah ya ce masa a cikin mafarki “I, na san ka yi wannan da kyakkyawan nufi, saboda haka ne na kiyaye ka daga yin mini zunubi. Shi ya sa ban bar ka ka taɓa ta ba.
7 Now then deliuer the man his wife againe: for he is a Prophet, and he shall pray for thee that thou mayest liue: but if thou deliuer her not againe, be sure that thou shalt die the death, thou, and all that thou hast.
Yanzu ka komar da matar mutumin, gama shi annabi ne, zai kuma yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In ba ka komar da ita ba fa, ka sani tabbatacce kai da dukan abin da yake naka za ku mutu.”
8 Then Abimelech rising vp early in ye morning, called all his seruants, and tolde all these things vnto them, and the men were sore afraid.
Kashegari da sassafe, sai Abimelek ya tara dukan fadawansa, ya faɗa musu duk abin da ya faru, suka ji tsoro ƙwarai da gaske.
9 Afterward Abimelech called Abraham, and said vnto him, What hast thou done vnto vs? and what haue I offeded thee, that thou hast brought on me and on my kingdome this great sinne? thou hast done things vnto me that ought not to be done.
Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
10 So Abimelech said vnto Abraham, What sawest thou that thou hast done this thing?
Abimelek ya kuma ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan?”
11 Then Abraham answered, Because I thought thus, Surely the feare of God is not in this place, and they will slay me for my wiues sake.
Ibrahim ya ce, “Na ce a raina, ‘Tabbatacce babu tsoron Allah a wannan wuri, za su kuwa kashe ni saboda matata.’
12 Yet in very deede she is my sister: for she is the daughter of my father, but not the daughter of my mother, and she is my wife.
Ban da haka, tabbatacce ita’yar’uwata ce,’yar mahaifina, ko da yake ba daga uwata ba, ta kuma zama matata.
13 Nowe when God caused me to wander out of my fathers house, I said then to her, This is thy kindnes that thou shalt shewe vnto me in all places where we come, Say thou of me, He is my brother.
Sa’ad da Allah ya sa na tashi daga gidan mahaifina na ce mata, ‘Wannan shi ne yadda za ki nuna mini ƙaunarki. Duk inda muka tafi, ki ce game da ni, “Shi ɗan’uwana ne.”’”
14 Then tooke Abimelech sheepe and beeues, and men seruants, and women seruants, and gaue them vnto Abraham, and restored him Sarah his wife.
Sai Abimelek ya kawo awaki da shanu da bayi maza da mata, ya ba wa Ibrahim, ya kuma komar da Saratu matarsa gare shi.
15 And Abimelech saide, Beholde, my land is before thee: dwell where it pleaseth thee.
Abimelek ya kuma ce, “Ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda kake so.”
16 Likewise to Sarah he said, Beholde, I haue giuen thy brother a thousand pieces of siluer: behold, he is the vaile of thine eyes to all that are with thee, and to all others: and she was thus reproued.
Ga Saratu kuwa ya ce, “Ina ba wa ɗan’uwanki shekel dubu na azurfa, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa cewa ba ki da laifi.”
17 Then Abraham prayed vnto God, and God healed Abimelech, and his wife, and his women seruants: and they bare children.
Sai Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuma ya warkar da Abimelek, da matarsa da bayinsa mata domin su haihu,
18 For the Lord had shut vp euery wombe of the house of Abimelech, because of Sarah Abrahams wife.
gama Ubangiji ya rufe kowace mahaifa a gidan Abimelek saboda Saratu, matar Ibrahim.

< Genesis 20 >