< Ezra 4 >

1 Bvt the aduersaries of Iudah and Beniamin heard, that the children of the captiuitie builded the Temple vnto the Lord God of Israel.
Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
2 And they came to Zerubbabel, and to the chiefe fathers, and sayd vnto them, We wil builde with you: for we seeke the Lord your God as ye do, and we haue sacrificed vnto him since the time of Esar Haddon king of Asshur, which brought vs vp hither.
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
3 Then Zerubbabel, and Ieshua, and the rest of the chiefe fathers of Israel, sayde vnto them, It is not for you, but for vs to buyld the house vnto our God: for we our selues together wil buylde it vnto the Lord God of Israel, as king Cyrus the king of Persia hath commanded vs.
Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
4 Wherefore the people of the land discouraged the people of Iudah, and troubled them in buylding,
Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
5 And they hired counsellers against them, to hinder their deuise, all the dayes of Cyrus King of Persia, euen vntill the reigne of Darius King of Persia.
Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
6 And in the reigne of Ahashuerosh (in the beginning of his reigne) wrote they an accusation against the inhabitants of Iudah and Ierusalem.
A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
7 And in the daies of Artahshashte, Mithredath, Tabeel, and the rest of their companions wrote when it was peace, vnto Artahshashte king of Persia, and the writing of the letter was the Aramites writing, and the thing declared was in the language of the Aramites.
A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
8 Rehum the chancelour, and Shimshai the scribe wrote a letter against Ierusalem to Artahshashte the King, in this sort.
Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
9 Then wrote Rehum the chauncelour, and Shimshai the scribe, and their companions Dinaie, and Apharsathcaie, Tarpelaie, Apharsaie, Archeuaie, Bablaie, Shushanchaie, Dehaue, Elmaie,
Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
10 And the rest of the people whom the great and noble Asnappar brought ouer, and set in the cities of Samaria, and other that are beyonde the Riuer and Cheeneth.
da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
11 This is the copie of the letter that they sent vnto King Artahshashte, THY SERVANTS the men beyond the Riuer and Cheeneth, salute thee.
(Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
12 Be it knowen vnto the King that ye Iewes, which came vp from thee to vs, are come vnto Ierusalem (a citie rebellious and wicked) and buylde, and lay the foundations of the walles, and haue ioyned the foundations.
Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
13 Be it knowen nowe vnto the King, that if this citie be built, and the foundations of the walles layed, they will not giue tolle, tribute, nor custome: so shalt thou hinder the Kings tribute.
Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
14 Nowe therefore because wee haue bene brought vp in the Kings palace, it was not meete for vs to see the Kings dishonour: for this cause haue we sent and certified the King,
Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
15 That one may searche in the booke of the Chronicles of thy fathers, and thou shalt finde in the booke of the Chronicles, and perceiue that this citie is rebellious and noysome vnto Kings and prouinces, and that they haue moued sedition of olde time, for the which cause this citie was destroyed.
domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
16 Wee certifie the King therefore, that if this citie be buylded, and the foundation of the walles layd, by this meanes the portion beyonde the Riuer shall not be thine.
Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
17 The King sent an answere vnto Rehum the Chauncelour, and Shimshai the Scribe, and so the rest of their companions that dwelt in Samaria, and vnto the other beyond the Riuer, Shelam and Cheeth.
Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
18 The letter which yee sent vnto vs, hath bene openly read before me,
An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
19 And I haue commanded and they haue searched, and founde, that this citie of olde time hath made insurrection against kings, and hath rebelled, and rebellion hath bene committed therein.
Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
20 There haue bene mightie kings also ouer Ierusalem, which haue ruled ouer all beyonde the Riuer, and tolle, tribute, and custome was giuen vnto them.
Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
21 Make ye now a decree, that those men may cease, and that the citie be not buylt, till I haue giuen another commandement.
Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
22 Take heede nowe that ye fayle not to doe this: why should domage grow to hurt the King?
Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
23 When the copie of king Artahshashtes letter was read before Rehum and Shimshai the scribe, and their companions, they went vp in all the haste to Ierusalem vnto the Iewes, and caused them to cease by force and power.
Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
24 Then ceased the worke of the house of God, which was in Ierusalem, and did stay vnto the second yeere of Darius King of Persia.
Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.

< Ezra 4 >