< Ecclesiastes 3 >

1 To all things there is an appointed time, and a time to euery purpose vnder the heauen.
Akwai lokaci domin kowane abu, da kuma lokaci domin kowane aiki a duniya.
2 A time to bee borne, and a time to die: a time to plant, and a time to plucke vp that which is planted.
Lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin shuki da lokacin tumɓukewa.
3 A time to slay, and a time to heale: a time to breake downe, and a time to builde.
Lokacin kisa da lokacin warkarwa, lokacin rushewa da lokacin ginawa.
4 A time to weepe, and a time to laugh: a time to mourne, and a time to dance.
Lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa.
5 A time to cast away stones, and a time to gather stones: a time to embrace, and a time to be farre from embracing.
Lokacin warwatsa duwatsu da lokacin tara su, lokacin runguma da lokacin dainawa.
6 A time to seeke, and a time to lose: a time to keepe, and a time to cast away.
Lokacin nema, da lokacin fid da zuciya, lokacin ajiyewa da lokacin zubarwa.
7 A time to rent, and a time to sowe: a time to keepe silence, and a time to speake.
Lokacin yagewa da lokacin ɗinkewa, lokacin yin shiru da lokacin magana.
8 A time to loue, and a time to hate: a time of warre, and a time of peace.
Lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.
9 What profite hath hee that worketh of the thing wherein he trauaileth?
Wace riba ce ma’aikaci yake da ita saboda wahalarsa?
10 I haue seene the trauaile that God hath giuen to ye sonnes of men to humble them thereby.
Na ga nawayar da Allah ya ɗora a kan mutane.
11 He hath made euery thing beautifull in his time: also he hath set the worlde in their heart, yet can not man finde out the worke that God hath wrought from the beginning euen to the end.
Ya yi kowane abu da kyau a lokacinsa. Ya kuma sa matuƙa a zukatan mutane, duk da haka sun kāsa gane abin da Allah ya yi daga farko zuwa ƙarshe.
12 I know that there is nothing good in them, but to reioyce, and to doe good in his life.
Na san ba abin da ya fi wa mutane kyau fiye da su ji daɗi su kuma yi alheri yayinda suke da rai.
13 And also that euery man eateth and drinketh, and seeth the commoditie of all his labour. this is the gift of God.
Cewa kowa yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗi cikin dukan aikinsa, wannan kyautar Allah ce.
14 I knowe that whatsoeuer God shall doe, it shalbe for euer: to it can no man adde, and from it can none diminish: for God hath done it, that they should feare before him.
Na san cewa duk abin da Allah ya yi zai dawwama har abada; ba abin da za a ƙara ko a rage. Allah ya yi haka domin mutane su girmama shi.
15 What is that that hath bene? that is nowe: and that that shalbe, hath now bene: for God requireth that which is past.
Duk abin da yana nan ya taɓa kasancewa, kuma abin da zai kasance, ya taɓa kasancewa; Allah kuma zai nemi bayanin abubuwan da suka wuce.
16 And moreouer I haue seene vnder the sunne the place of iudgement, where was wickednesse, and the place of iustice where was iniquitie.
Sai na ga wani abu kuma a duniya, a wurin shari’a, akwai mugunta a can, a wurin adalci, akwai mugunta a can.
17 I thought in mine heart, God wil iudge the iust and the wicked: for time is there for euery purpose and for euery worke.
Sai na yi tunani a zuciyata, “Allah zai shari’anta masu adalci da masu mugunta, gama za a kasance da lokaci domin kowane aiki, lokaci domin kowane abu.”
18 I considered in mine heart the state of the children of men that God had purged them: yet to see to, they are in themselues as beastes.
Na sāke yin tunani, “Game da mutane kam, Allah kan gwada su don su san cewa ba su fi dabba ba.
19 For the condition of the children of men, and the condition of beasts are euen as one condition vnto them. As the one dyeth, so dyeth the other: for they haue all one breath, and there is no excellency of man aboue ye beast: for all is vanitie.
Ƙaddarar mutum ɗaya take da ta dabba; ƙaddara ɗaya ce take jiransu biyu. Yadda ɗayan yake mutuwa, haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne; mutum bai fi dabba ba. Kowane abu ba shi da amfani.
20 All goe to one place, and all was of the dust, and all shall returne to the dust.
Duka wuri ɗaya za su tafi; gama duka daga turɓaya suka fito, kuma ga turɓaya duka za su koma.
21 Who knoweth whether the spirit of man ascend vpward, and the spirit of the beast descend downeward to the earth?
Wa ya tabbatar cewa ruhun mutum yakan tashi sama sa’an nan na dabba yă sauka ƙasa?”
22 Therefore I see that there is nothing better then that a man shoulde reioyce in his affaires, because that is his portion. For who shall bring him to see what shalbe after him?
Saboda haka na ga babu abin da ya fi kyau wa mutum fiye da yă more wahalar aikinsa, domin wannan ne rabonsa. Gama wa zai kawo shi yă ga abin da zai faru a bayansa?

< Ecclesiastes 3 >