< Deuteronomy 1 >

1 These bee the wordes which Moses spake vnto all Israel, on this side Iorden in the wildernesse, in the plaine, ouer against the red Sea, betweene Paran and Tophel, and Laban, and Hazeroth, and Di-zahab.
Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
2 There are eleuen dayes iourney from Horeb vnto Kadesh-barnea, by the way of mout Seir.
(Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
3 And it came to passe in the first day of the eleuenth moneth, in the fourtieth yeere that Moses spake vnto the children of Israel according vnto all that the Lord had giuen him in commandement vnto them,
A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
4 After that he had slaine Sihon the king of the Amorites which dwelt in Heshbon, and Og king of Bashan, which dwelt at Ashtaroth in Edrei.
Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
5 On this side Iorden in the lande of Moab began Moses to declare this lawe, saying,
Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
6 The Lord our God spake vnto vs in Horeb, saying, Ye haue dwelt long ynough in this mount,
Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
7 Turne you and depart, and goe vnto the mountaine of the Amorites, and vnto all places neere thereunto in the plaine, in the mountaine, or in the valley: both Southwarde, and to the Sea side, to the land of the Canaanites, and vnto Lebanon: euen vnto the great riuer, the riuer Perath.
Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
8 Beholde, I haue set the land before you: go in and possesse that land which the Lord sware vnto your fathers, Abraham, Izhak, and Iaakob, to giue vnto them and to their seede after them.
Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
9 And I spake vnto you the same time, saying, I am not able to beare you my selfe alone:
A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
10 The Lord your God hath multiplied you: and beholde, ye are this day as the starres of heauen in nomber:
Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
11 (The Lord God of your fathers make you a thousand times so many moe as ye are, and blesse you, as he hath promised you)
Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
12 Howe can I alone beare your combrance and your charge, and your strife?
Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
13 Bring you men of wisedome and of vnderstanding, and knowen among your tribes, and I will make them rulers ouer you:
Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
14 Then ye answered me and said, The thing is good that thou hast commanded vs to doe.
Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
15 So I tooke the chiefe of your tribes wise and knowen men, and made them rulers ouer you, captaines ouer thousands, and captaines ouer hundreds, and captaines ouer fiftie, and captaines ouer tenne, and officers among your tribes.
Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
16 And I charged your iudges that same time, saying, Heare the controuersies betweene your brethren, and iudge righteously betweene euery man and his brother, and the stranger that is with him.
Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
17 Ye shall haue no respect of person in iudgement, but shall heare the small aswell as the great: yee shall not feare the face of man: for the iudgement is Gods: and the cause that is too hard for you, bring vnto me, and I will heare it.
Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
18 Also I commanded you the same time all the things which ye should doe.
A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
19 Then we departed from Horeb, and went through all that great and terrible wildernesse (as yee haue seene) by the way of the mountaine of the Amorites, as the Lord our God commanded vs: and we came to Kadesh-barnea.
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
20 And I saide vnto you, Yee are come vnto the mountaine of the Amorites, which the Lord our God doeth giue vnto vs.
Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
21 Beholde, the Lord thy God hath layde the land before thee: go vp and possesse it, as the Lord the God of thy fathers hath saide vnto thee: feare not, neither be discouraged.
Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
22 Then ye came vnto me euery one, and said, We wil send men before vs, to search vs out the land and to bring vs word againe, what way we must go vp by, and vnto what cities we shall come.
Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
23 So the saying pleased me well, and I tooke twelue men of you, of euery tribe one.
Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
24 Who departed, and went vp into the mountaine, and came vnto the riuer Eshcol, and searched out the land.
Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
25 And tooke of the fruite of the land in their hands, and brought it vnto vs, and brought vs worde againe, and sayd, It is a good land, which the Lord our God doeth giue vs.
Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
26 Notwithstanding, ye would not go vp, but were disobedient vnto the commandement of the Lord your God,
Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
27 And murmured in your tentes, and sayd, Because the Lord hated vs, therefore hath hee brought vs out of the land of Egypt, to deliuer vs into the hand of the Amorites, and to destroy vs.
Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
28 Whither shall we go vp? our brethren haue discouraged our hearts, saying, The people is greater, and taller then we: the cities are great and walled vp to heauen: and moreouer we haue seene the sonnes of the Anakims there.
Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
29 But I sayd vnto you, Dread not, nor be afrayd of them.
Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
30 The Lord your God, who goeth before you, he shall fight for you, according to all that he did vnto you in Egypt before your eyes,
Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
31 And in the wildernesse, where thou hast seene how the Lord thy God bare thee, as a man doeth beare his sonne, in all the way which ye haue gone, vntill ye came vnto this place.
da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 Yet for all this ye did not beleeue the Lord your God,
Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
33 Who went in the way before you, to search you out a place to pitch your tentes in, in fire by night, that ye might see what way to goe, and in a cloude by day.
shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
34 Then the Lord heard the voyce of your wordes, and was wroth, and sware, saying,
Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
35 Surely there shall not one of these men of this froward generation, see that good land, which I sware to giue vnto your fathers,
“Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
36 Saue Caleb the sonne of Iephunneh: he shall see it, and to him will I giue the land that he hath troden vpon, and to his children, because he hath constantly followed the Lord.
sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Also the Lord was angry with me for your sakes, saying, Thou also shalt not goe in thither,
Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
38 But Ioshua the sonne of Nun which standeth before thee, he shall go in thither: incourage him: for he shall cause Israel to inherite it.
Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
39 Moreouer, your children, which ye sayd should be a praye, and your sonnes, which in that day had no knowledge betweene good and euill, they shall go in thither, and vnto them wil I giue it, and they shall possesse it.
Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
40 But as for you, turne backe, and take your iourney into the wildernesse by the way of the red Sea.
Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
41 Then ye answered and sayd vnto me, We haue sinned against the Lord, we wil go vp, and fight, according to all that the Lord our God hath commanded vs: and ye armed you euery man to the warre, and were ready to goe vp into the mountaine.
Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
42 But the Lord said vnto me, Say vnto them, Goe not vp, neither fight, (for I am not among you) least ye fall before your enemies.
Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
43 And when I told you, ye would not heare, but rebelled against the commandement of the Lord, and were presumptuous, and went vp into the mountaine.
Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
44 Then the Amorites which dwelt in that mountaine came out against you, and chased you (as bees vse to doe) and destroied you in Seir, euen vnto Hormah.
Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
45 And when ye came againe, ye wept before the Lord, but the Lord would not heare your voyce, nor incline his eares vnto you.
Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
46 So ye abode in Kadesh a long time, according to the time that ye had remained before.
Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.

< Deuteronomy 1 >