< Deuteronomy 2 >

1 Then we turned, and tooke our iourney into the wildernes, by the way of the red Sea, as the Lord spake vnto me: and we compassed mount Seir a long time.
Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
2 And the Lord spake vnto me, saying,
Sai Ubangiji ya ce mini,
3 Ye haue compassed this mountaine long ynough: turne you Northward.
“Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
4 And warne thou the people, saying, Ye shall go through the coast of your brethren the children of Esau, which dwell in Seir, and they shall be afraide of you: take ye good heede therefore.
Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
5 Ye shall not prouoke them: for I wil not giue you of their land so much as a foot breadth, because I haue giuen mount Seir vnto Esau for a possession.
kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
6 Ye shall buy meate of them for money to eate, and ye shall also procure water of them for money to drinke.
Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
7 For the Lord thy God hath blessed thee in all the workes of thine hand: he knoweth thy walking through this great wildernes, and the Lord thy God hath bene with thee this fourtie yeere, and thou hast lacked nothing.
Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
8 And when we were departed from our brethren the children of Esau which dwelt in Seir, through the way of the plaine, from Elath, and from Ezion-gaber, we turned and went by the way of the wildernes of Moab.
Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
9 Then the Lord sayd vnto me, Thou shalt not vexe Moab, neither prouoke them to battel: for I wil not giue thee of their land for a possession, because I haue giuen Ar vnto the children of Lot for a possession.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
10 The Emims dwelt therein in times past, a people great and many, and tall, as the Anakims.
(Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
11 They also were taken for gyants as the Anakims: whom the Moabites call Emims.
Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
12 The Horims also dwelt in Seir before time, whome the children of Esau chased out and destroyed them before them, and dwelt in their steade: as Israel shall doe vnto the land of his possession, which the Lord hath giuen them.
Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
13 Now rise vp, sayd I, and get you ouer the riuer Zered: and we went ouer the riuer Zered.
Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
14 The space also wherein we came from Kadesh-barnea, vntill we were come ouer the riuer Zered, was eight and thirtie yeeres, vntill all the generation of the men of warre were wasted out from among the hoste, as the Lord sware vnto them.
Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
15 For in deede the hand of the Lord was against them, to destroy them from among the hoste, till they were consumed.
Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
16 So when all the men of warre were consumed and dead from among the people:
To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
17 Then the Lord spake vnto me, saying,
sai Ubangiji ya ce mini,
18 Thou shalt goe through Ar the coast of Moab this day:
“Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
19 And thou shalt come neere ouer against the children of Ammon: but shalt not lay siege vnto them, nor moue warre against them: for I will not giue thee of the land of the children of Ammon any possession: for I haue giuen it vnto the children of Lot for a possession.
Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
20 That also was taken for a land of gyants: for gyants dwelt therein afore time, whome the Ammonites called Zamzummims:
(Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
21 A people that was great, and many, and tall, as the Anakims: but the Lord destroyed them before them, and they succeeded them in their inheritance, and dwelt in their stead:
Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
22 As he did to the children of Esau which dwell in Seir, when he destroyed the Horims before them, and they possessed them, and dwelt in their stead vnto this day.
Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
23 And the Auims which dwelt in Hazarim euen vnto Azzah, the Caphtorims which came out of Caphtor destroyed them, and dwelt in their steade.
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
24 Rise vp therefore, sayd the Lord: take your iourney, and passe ouer the riuer Arnon: beholde, I haue giuen into thy hand Sihon, the Amorite, King of Heshbon, and his land: begin to possesse it and prouoke him to battell.
“Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
25 This day wil I begin to send thy feare and thy dread, vpon all people vnder the whole heauen, which shall heare thy fame, and shall tremble and quake before thee.
A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
26 Then I sent messengers out of the wildernes of Kedemoth vnto Sihon King of Heshbon, with wordes of peace, saying,
Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
27 Let me passe through thy land: I will go by the hie way: I will neither turne vnto the right hand nor to the left.
“Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
28 Thou shalt sell me meate for money, for to eate, and shalt giue me water for money for to drinke: onely I will go through on my foote,
Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
29 (As the children of Esau which dwell in Seir, and the Moabites which dwell in Ar, did vnto me) vntill I be come ouer Iorden, into the land which the Lord our God giueth vs.
kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
30 But Sihon the King of Heshbon would not let vs passe by him: for the Lord thy God had hardened his spirit, and made his heart obstinate, because hee would deliuer him into thine hand, as appeareth this day.
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
31 And the Lord sayd vnto me, Beholde, I haue begun to giue Sihon and his land before thee: begin to possesse and inherite his land.
Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
32 Then came out Sihon to meete vs, him selfe with all his people to fight at Iahaz.
Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
33 But the Lord our God deliuered him into our power, and we smote him, and his sonnes, and all his people.
sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
34 And we tooke all his cities the same time, and destroyed euery citie, men, and women, and children: we let nothing remaine.
A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 Onely the cattell we tooke to our selues, and the spoyle of the cities which we tooke,
Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
36 From Aroer, which is by the banke of the riuer of Arnon, and from the citie that is vpon the riuer, euen vnto Gilead: there was not one citie that escaped vs: for the Lord our God deliuered vp all before vs.
Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
37 Onely vnto the land of the children of Ammon thou camest not, nor vnto any place of the riuer Iabbok, nor vnto the cities in the mountaines, nor vnto whatsoeuer the Lord our God forbade vs.
Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.

< Deuteronomy 2 >