< 2 Samuel 7 >

1 Afterwarde when the King sate in his house and the Lord had giuen him rest rounde about from all his enemies,
Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
2 The King saide vnto Nathan the Prophet, Beholde, nowe I dwel in an house of cedar trees, and the Arke of God remayneth within the curtaines.
sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
3 Then Nathan sayde vnto the King, Go, and doe all that is in thine heart: for the Lord is with thee.
Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
4 And the same night the worde of the Lord came vnto Nathan, saying,
A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
5 Goe and tell my seruant Dauid, Thus saieth the Lord, Shalt thou buylde me an house for my dwelling?
“Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
6 For I haue dwelt in no house since the time that I brought the children of Israel out of Egypt vnto this day, but haue walked in a tent and tabernacle.
Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
7 In al the places wherein I haue walked with all the children of Israel, spake I one worde with any of the tribes of Israel when I commanded the iudges to feede my people Israel? or sayde I, Why build ye not me an house of cedar trees?
A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
8 Nowe therefore so say vnto my seruant Dauid, Thus saieth the Lord of hostes, I tooke thee from the sheepecote following the sheepe, that thou mightest bee ruler ouer my people, ouer Israel.
“Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
9 And I was with thee wheresoeuer thou hast walked, and haue destroyed all thine enemies out of thy sight, and haue made thee a great name, like vnto the name of the great men that are in the earth.
Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
10 (Also I will appoynt a place for my people Israel, and will plant it, that they may dwell in a place of their owne, and moue no more, neither shall wicked people trouble them any more as before time,
Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
11 And since the time that I set Iudges ouer my people of Israel) and I will giue thee rest from al thine enemies: also the Lord telleth thee, that he will make thee an house.
yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
12 And when thy daies bee fulfilled, thou shalt sleepe with thy fathers, and I wil set vp thy seede after thee, which shall proceede out of thy body, and will stablish his kingdome.
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
13 He shall buyld an house for my Name, and I will stablish ye throne of his kingdome for euer.
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
14 I will be his father, and hee shall bee my sonne: and if he sinne, I will chasten him with the rod of men, and with the plagues of the children of men.
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
15 But my mercy shall not depart away from him, as I tooke it from Saul whome I haue put away before thee.
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
16 And thine house shall be stablished and thy kingdome for euer before thee, euen thy throne shalbe stablished for euer.
Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
17 According to all these wordes, and according to all this vision, Nathan spake thus vnto Dauid.
Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
18 Then King Dauid went in, and sate before the Lord, and sayde, Who am I, O Lord God, and what is mine house, that thou hast brought me hitherto?
Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
19 And this was yet a small thing in thy sight, O Lord God, therefore thou hast spoken also of thy seruants house for a great while: but doth this appertaine to man, O Lord God?
Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
20 And what can Dauid say more vnto thee? for thou, Lord God, knowest thy seruant.
“Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
21 For thy words sake, and according to thine owne heart hast thou done all these great things, to make them knowen vnto thy seruant.
Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
22 Wherefore thou art great, O Lord God: for there is none like thee, neither is there any God besides thee, according to all that wee haue heard with our eares.
“Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
23 And what one people in the earth is like thy people, like Israel? whose God went and redeemed them to himselfe, that they might be his people, and that hee might make him a name, and do for you great things, and terrible for thy land, O Lord, euen for thy people, whome thou redeemedst to thee out of Egypt, from the nations, and their gods?
Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
24 For thou hast ordeyned to thy selfe thy people Israel to be thy people for euer: and thou Lord art become their God.
Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
25 Nowe therefore, O Lord God, confirme for euer the word that thou hast spoken concerning thy seruant and his house, and doe as thou hast sayde.
“Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
26 And let thy Name bee magnified for euer by them that shall say, The Lord of hostes is the God ouer Israel: and let the house of thy seruant Dauid be stablished before thee.
domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
27 For thou, O Lord of hostes, God of Israel, hast reueiled vnto thy seruant, saying, I will build thee an house: therefore hath thy seruant bene bold to pray this prayer vnto thee.
“Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
28 Therefore now, O Lord God, (for thou art God, and thy words be true, and thou hast tolde this goodnes vnto thy seruant)
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
29 Therefore nowe let it please thee to blesse the house of thy seruant, that it may continue for euer before thee: for thou, O Lord God, hast spoken it: and let the house of thy seruant be blessed for euer, with thy blessing.
In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”

< 2 Samuel 7 >