< 2 Samuel 6 >

1 Againe Dauid gathered together all the chosen men of Israel, euen thirtie thousand,
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 And Dauid arose and went with all the people that were with him from Baale of Iudah to bring vp from thence the Arke of God, whose name is called by the Name of the Lord, of hostes, that dwelleth vpon it betweene the Cherubims.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 And they put the Arke of God vpon a newe cart, and brought it out of the house of Abinadab that was in Gibeah. And Vzzah and Ahio the sonnes of Abinadab did driue the newe carte.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 And when they brought the Arke of God out of the house of Abinadab, that was at Gibeah, Ahio went before the Arke,
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 And Dauid and al the house of Israel played before the Lord on all instruments made of firre, and on harpes, and on Psalteries, and on timbrels, and on cornets, and on cymbals.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 And when they came to Nachons threshing floore, Vzzah put his hande to the Arke of God, and helde it: for the oxen did shake it.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 And the Lord was verie wroth with Vzzah, and God smote him in the same place for his fault, and there he dyed by the Arke of God.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 And Dauid was displeased, because the Lord had smitten Vzzah: and he called the name of the place Perez Vzzah vntill this day.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 Therefore Dauid that day feared the Lord, and sayd, How shall the Arke of the Lord come to mee?
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 So Dauid would not bring the Arke of the Lord vnto him into the citie of Dauid, but Dauid caried it into ye house of Obed-edom a Gittite.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 And the Arke of the Lord continued in the house of Obed-edom the Gittite, three moneths, and the Lord blessed Obed-edom, and all his houshold.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 And one told King Dauid, saying, The Lord hath blessed the house of Obed-edom, and all that hee hath, because of the Arke of God: therefore Dauid went and brought the Arke of God from the house of Obed-edom, into the citie of Dauid with gladnesse.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 And when they that bare the Arke of the Lord had gone sixe paces, he offred an oxe, and a fatte beast.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 And Dauid danced before the Lord with al his might, and was girded with a linnen Ephod.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 So Dauid and all the house of Israel, brought the Arke of the Lord with shouting, and sound of trumpet.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 And as the Arke of the Lord came into the citie of Dauid, Michal Sauls daughter looked through a windowe, and sawe King Dauid leape, and dance before the Lord, and shee despised him in her heart.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 And when they had brought in the Arke of the Lord, they set it in his place, in the mids of the tabernacle that Dauid had pitched for it: then Dauid offred burnt offrings, and peace offrings before the Lord.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 And assoone as Dauid had made an ende of offring burnt offrings and peace offrings, hee blessed the people in the Name of the Lord of hostes,
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 And gaue among all the people, euen among the whole multitude of Israel, aswel to the women as men, to euerie one a cake of bread, and a piece of flesh, and a bottell of wine: so all the people departed euerie one to his house.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 The Dauid returned to blesse his house, and Michal the daughter of Saul came out to meete Dauid, and sayde, O howe glorious was the King of Israel this day, which was vncouered to day in the eyes of the maidens of his seruantes, as a foole vncouereth himselfe.
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 Then Dauid sayd vnto Michal, It was before the Lord, which chose me rather then thy father, and all his house, and commanded me to bee ruler ouer the people of the Lord, euen ouer Israel: and therefore will I play before the Lord,
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 And will yet be more vile then thus, and will be low in mine owne sight, and of the verie same maidseruants, which thou hast spoken of, shall I be had in honour.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Therfore Michal the daughter of Saul had no childe vnto the day of her death.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >