< 2 Samuel 18 >

1 Then Dauid numbred the people that were with him, and set ouer them captaines of thousands and captaines of hundreths.
Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
2 And Dauid sent foorth the third part of the people vnder the hand of Ioab, and the thirde part vnder the hand of Abishai Ioabs brother the sonne of Zeruiah: and the other third part vnder the hand of Ittai the Gittite. and the King said vnto the people, I will go with you my selfe also.
Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
3 But the people answered, Thou shalt not goe foorth: for if we flee away, they will not regarde vs, neither will they passe for vs, though halfe of vs were slaine: but thou art now worth ten thousande of vs: therefore nowe it is better that thou succour vs out of the citie.
Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
4 Then the King said vnto them, What seemeth you best, that I will doe. So the King stood by the gate side, and all the people came out by hundreths and by thousands.
Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
5 And the King commanded Ioab and Abishai, and Ittai, saying, Entreate the yong man Absalom gently for my sake. and all the people heard whe the King gaue al the captaines charge concerning Absalom.
Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
6 So the people went out into the fielde to meete Israel, and the battell was in the wood of Ephraim:
Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
7 Where the people of Israel were slaine before the seruants of Dauid: so there was a great slaughter that day, euen of twentie thousande.
A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
8 For the battel was skattered ouer all the countrey: and the wood deuoured much more people that day, then did the sworde.
Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
9 Nowe Absalom met the seruants of Dauid, and Absalom rode vpon a mule, and the mule came vnder a great thicke oke: and his head caught holde of the oke, and he was taken vp betweene the heauen and the earth: and the mule that was vnder him went away.
To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
10 And one that sawe it, tolde Ioab, saying, Beholde, I sawe Absalom hanged in an oke.
Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
11 Then Ioab saide vnto the man that tolde him, And hast thou in deede seene? why then diddest thou not there smite him to the grounde, and I woulde haue giuen thee ten shekels of siluer, and a girdle?
Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
12 Then the man saide vnto Ioab, Though I should receiue a thousande shekels of siluer in mine hande, yet woulde I not lay mine hande vpon the Kings sonne: for in our hearing the King charged thee, and Abishai, and Ittai, saying, Beware, least any touche the yong man Absalom.
Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
13 If I had done it, it had bene the danger of my life: for nothing can be hid from the King: yea, thou thy selfe wouldest haue bin against me.
Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
14 Then saide Ioab, I will not thus tary with thee. And he tooke three dartes in his hande, and thrust them through Absalom, while he was yet aliue in the middes of the oke.
Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
15 And tenne seruants that bare Ioabs armour, compassed about and smote Absalom, and slewe him.
Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
16 Then Ioab blewe the trumpet, and the people returned from pursuing after Israel: for Ioab helde backe the people.
Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
17 And they tooke Absalom, and cast him into a great pit in the wood, and layed a mightie great heape of stones vpon him: and all Israel fled euery one to his tent.
Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
18 Nowe Absalom in his life time had taken and reared him vp a pillar, which is in the kings dale: for he saide, I haue no sonne to keepe my name in remembrance. and he called the pillar after his owne name, and it is called vnto this day, Absaloms place.
A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
19 Then said Ahimaaz the sonne of Zadok, I pray thee, let me runne, and beare the King tidings that the Lord hath deliuered him out of the hande of his enemies.
Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
20 And Ioab said vnto him, Thou shalt not be the messenger to day, but thou shalt beare tidings another time, but to day thou shalt beare none: for the Kings sonne is dead.
Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
21 Then said Ioab to Cushi, Goe, tel the king, what thou hast seene. And Cushi bowed himselfe vnto Ioab, and ran.
Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
22 Then saide Ahimaaz the sonne of Zadok againe to Ioab, What, I pray thee, if I also runne after Cushi? And Ioab said, Wherefore now wilt thou runne, my sonne, seeing that thou hast no tidings to bring?
Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
23 Yet what if I runne? Then he saide vnto him, Runne. So Ahimaaz ranne by the way of the plaine, and ouerwent Cushi.
Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
24 Now Dauid sate betweene the two gates. And the watchman went to the top of the gate vpon the wall, and lift vp his eyes, and sawe, and beholde, a man came running alone.
Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
25 And the watchman cryed, and tolde ye king. And the King said, If he be alone, he bringeth tidings. And he came apace, and drew neere.
Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
26 And the watchman saw another man running, and the watchman called vnto the porter, and said, Behold, another man runneth alone. And the King said, He also bringeth tidings.
Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
27 And the watchman said, Me thinketh the running of the formost is like the running of Ahimaaz the sonne of Zadok. Then the King said, He is a good man, and commeth with good tidings.
Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
28 And Ahimaaz called, and sayde vnto the King, Peace be with thee: and he fell downe to the earth vpon his face before the King, and saide, Blessed be the Lord thy God, who hath shut vp the men that lift vp their handes against my lorde the King.
Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
29 And the King saide, Is the yong man Absalom safe? And Ahimaaz answered, When Ioab sent the Kings seruant, and me thy seruant, I sawe a great tumult, but I knewe not what.
Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
30 And the King said vnto him, Turne aside, and stand here. so he turned aside and stoode still.
Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
31 And beholde, Cushi came, and Cushi saide, Tidings, my lorde the King: for the Lord hath deliuered thee this day out of the hande of all that rose against thee.
Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
32 Then the King saide vnto Cushi, Is the yong man Absalom safe? And Cushi answered, The enemies of my lorde the King, and all that rise against thee to doe thee hurt, be as that yong man is.
Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
33 And the King was mooued, and went vp to the chamber ouer the gate, and wept: and as he went, thus he said, O my sonne Absalom, my sonne, my sonne Absalom: woulde God I had dyed for thee, O Absalom, my sonne, my sonne.
Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”

< 2 Samuel 18 >