< 2 Kings 25 >

1 And in the ninth yeere of his reigne, the tenth moneth and tenth day of the moneth Nebuchad-nezzar King of Babel came, he, and all his hoste against Ierusalem, and pitched against it, and they built fortes against it round about it.
A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
2 So the citie was besieged vnto the eleueth yeere of King Zedekiah.
Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
3 And the ninth day of the moneth the famine was sore in the citie, so that there was no bread for the people of the lande.
A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
4 Then the citie was broken vp, and all the men of warre fled by night, by the way of the gate, which is betweene two walles that was by the Kings garden: nowe the Caldees were by the citie round about: and the King went by the way of the wildernesse.
Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
5 But the armie of the Caldees pursued after the King, and tooke him in the desertes of Iericho, and all his hoste was scattered from him.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
6 Then they tooke the King, and caried him vp to the King of Babel to Riblah, where they gaue iudgement vpon him.
Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
7 And they slew the sonnes of Zedekiah before his eyes, and put out the eyes of Zedekiah, and bounde him in chaines, and caried him to Babel.
Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
8 And in the fift moneth, and seuenth day of the moneth, which was the nineteenth yere of King Nebuchad-nezzar King of Babel, came Nebuzar-adan chiefe stewarde and seruaunt of the King of Babel, to Ierusalem,
A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
9 And burnt the house of the Lord, and the Kings house, and all the houses of Ierusalem, and all the great houses burnt he with fire.
Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
10 And all the armie of the Caldees that were with the chiefe stewarde, brake downe the walles of Ierusalem round about.
Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
11 And the rest of the people that were left in the citie, and those that were fled and fallen to the King of Babel, with the remnant of the multitude, did Nebuzar-adan chiefe steward carie away captiue.
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
12 But the chiefe steward left of the poore of the land to dresse the vines, and to till the land.
Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
13 Also the pillars of brasse that were in the house of the Lord, and the bases, and the brasen Sea that was in the house of the Lord, did the Caldees breake, and caried the brasse of them to Babel.
Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
14 The pots also and the besomes, and the instruments of musike, and the incense dishes, and al the vessels of brasse that they ministred in, tooke they away.
Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
15 And the asshe pannes, and the basens, and all that was of gold, and that was of siluer, tooke the chiefe steward away,
Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
16 With the two pillars, one Sea and the bases, which Salomon had made for the house of the Lord: the brasse of all these vessels was without weight.
Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
17 The height of the one pillar was eighteene cubits, and the chapiter thereon was brasse, and the height of the chapiter was with networke three cubites, and pomegranates vpon the chapiter rounde about, all of brasse: and likewise was the second pillar with the networke.
Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
18 And the chiefe steward tooke Seraiah the chiefe Priest, and Zephaniah the second Priest, and the three keepers of the doore.
Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
19 And out of the citie hee tooke an Eunuch that had the ouersight of the men of warre, and fiue men of them that were in the Kinges presence, which were founde in the citie, and Sopher captaine of the hoste, who mustred the people of the lande, and threescore men of the people of the lande, that were founde in the citie.
Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
20 And Nebuzar-adan the chiefe stewarde tooke them, and brought them to the King of Babel to Riblah.
Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
21 And the King of Babel smote them, and slew them at Riblah in the land of Hamath. So Iudah was caried away captiue out of his owne land.
A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
22 Howbeit there remained people in the land of Iudah, whom Nebuchad-nezzar King of Babel left, and made Gedaliah the sonne of Ahikam the sonne of Shaphan ruler ouer them.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
23 Then when all the captaines of the host and their men heard, that the king of Babel had made Gedaliah gouernour, they came to Gedaliah to Mizpah, to wit, Ishmael the sonne of Nethaniah, and Iohanan the sonne of Kareah, and Seraiah the sonne of Tanhumeth the Netophathite, and Iaazaniah the sonne of Maachathi, they and their men.
Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
24 And Gedaliah sware to them, and to their men, and sayd vnto them, Feare not to be the seruants of the Caldees: dwell in the land, and serue the King of Babel, and ye shalbe well.
Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
25 But in the seuenth moneth Ishmael the sonne of Nethaniah the sonne of Elishama of the Kings seede, came, and ten men with him, and smote Gedaliah, and he died, and so did he the Iewes, and the Caldees that were with him at Mizpah.
Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
26 Then all ye people both small and great, and the captaines of the armie arose, and came to Egypt: for they were afraide of the Caldees.
Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
27 Notwithstanding in the seuen and thirtieth yeere after Iehoiachin King of Iudah was caried away, in the twelft moneth and the seuen and twentieth day of the moneth, Euil-merodach King of Babel in the yeere that hee began to reigne, did lift vp the head of Iehoiachin King of Iudah out of the prison,
A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
28 And spake kindly to him, and set his throne aboue the throne of the Kings that were with him in Babel,
Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
29 And changed his prison garments: and he did continually eate bread before him, all the dayes of his life.
Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
30 And his portion was a continual portion giuen him by the King, euery day a certaine, all the dayes of his life.
Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.

< 2 Kings 25 >