< 2 Kings 22 >

1 Iosiah was eight yeere olde when he beganne to reigne, and hee reigned one and thirtie yeere in Ierusalem. His mothers name also was Iedidah the daughter of Adaiah of Bozcath.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 And hee did vprightly in the sight of the Lord, and walked in all the wayes of Dauid his father, and bowed neither to the right hand, nor to the left.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 And in the eighteenth yeere of King Iosiah, the King sent Shaphan the sonne of Azaliah the sonne of Meshullam the chanceller to ye house of the Lord, saying,
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 Goe vp to Hilkiah the high Priest, that hee may summe the siluer which is brought into the house of the Lord, which the keepers of the doore haue gathered of the people.
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 And let them deliuer it into the hande of them that doe the worke, and haue the ouersight of the house of the Lord: let them giue it to them that worke in the house of the Lord, to repaire the decayed places of the house:
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 To wit, vnto the artificers and carpenters and masons, and to bye timber, and hewed stone to repaire the house.
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 Howebeit, let no rekoning bee made with them of the money, that is deliuered into their hand: for they deale faithfully.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 And Hilkiah the high Priest sayde vnto Shaphan the chanceller, I haue found the booke of the Lawe in the house of the Lord: and Hilkiah gaue the booke to Shaphan, and hee reade it.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 So Shaphan the chanceller came to ye King, and brought him word againe, and saide, Thy seruants haue gathered the money, that was found in the house, and haue deliuered it vnto the hands of them that doe the worke, and haue the ouersight of the house of the Lord.
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 Also Shaphan the chanceller shewed the King saying, Hilkiah the Priest hath deliuered me a booke. And Shaphan read it before the King.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 And when the King had heard the wordes of the booke of the Law, he rent his clothes.
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 Therefore the King commanded Hilkiah the Priest, and Ahikam the sonne of Shaphan, and Achbor the sonne of Michaiah, and Shaphan the chanceller, and Asahiah the Kings seruant, saying,
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 Go ye and inquire of the Lord for me, and for the people, and for all Iudah concerning the wordes of this booke that is founde: for great is the wrath of the Lord that is kindled against vs, because our fathers haue not obeyed the wordes of this booke, to doe according vnto all that which is written therein for vs.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 So Hilkiah the Priest and Ahikam, and Achbor and Shaphan, and Asahiah went vnto Huldah the Prophetesse the wife of Shallum, ye sonne of Tikuah, the sonne of Harhas keeper of the wardrobe: (and she dwelt in Ierusalem in the colledge) and they communed with her.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 And shee answered them, Thus sayth the Lord God of Israel, Tel the man that sent you to mee,
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 Thus sayth the Lord, Behold, I wil bring euill vpon this place, and on the inhabitants thereof, euen al the words of the booke which ye King of Iudah hath read,
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 Because they haue forsaken mee, and haue burnt incense vnto other gods, to anger me with all ye works of their hands: my wrath also shalbe kindled against this place and shall not be queched:
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 But to the King of Iudah, who sent you to inquire of the Lord, so shall ye say vnto him, Thus sayeth the Lord God of Israel, The wordes that thou hast heard, shall come to passe.
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 But because thine heart did melt, and thou hast humbled thy selfe before the Lord, when thou heardest what I spake against this place, and against the inhabitants of the same, to wit, that it should be destroyed and accursed, and hast rent thy clothes, and wept before me, I haue also heard it, saith the Lord.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Beholde therefore, I wil gather thee to thy fathers, and thou shalt be put in thy graue in peace, and thine eyes shall not see all the euil, which I will bring vpon this place. Thus they brought the King worde againe.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Kings 22 >