< 2 Kings 14 >

1 The second yeere of Ioash sonne of Iehoahaz King of Israel reigned Amaziah the sonne of Ioash King of Iudah.
A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 He was fiue and twentie yeere olde when he began to reigne, and reigned nine and twentie yeere in Ierusalem, and his mothers name was Iehoadan of Ierusalem.
Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
3 And he did vprightly in the sight of the Lord, yet not like Dauid his father, but did according to all that Ioash his father had done.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
4 Notwithstanding the hie places were not taken away: for as yet the people did sacrifice and burnt incense in the hie places.
Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
5 And when the kingdome was confirmed in his hand, he slewe his seruants which had killed the King his father.
Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
6 But the children of those that did slay him, he slewe not, according vnto that that is written in the booke of the Lawe of Moses, wherein the Lord commanded, saying, The fathers shall not be put to death for the children, nor the children put to death for the fathers: but euery man shall be put to death for his owne sinne.
Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
7 He slew also of Edom in the valley of salt ten thousand, and tooke the citie of Sela by warre, and called the name thereof Ioktheel vnto this day.
Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
8 Then Amaziah sent messengers to Iehoash the sonne of Iehoahaz, sonne of Iehu King of Israel, saying, Come, let vs see one another in the face.
Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
9 Then Iehoash the King of Israel sent to Amaziah King of Iudah, saying, The thistle that is in Lebanon, sent to the cedar that is in Lebanon, saying, Giue thy daughter to my sonne to wife: and the wilde beast that was in Lebanon, went and trode downe the thistle.
Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
10 Because thou hast smitten Edom, thine heart hath made thee proud: bragge of glory, and tary at home. why doest thou prouoke to thine hurt, that thou shouldest fall, and Iudah with thee?
Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
11 But Amaziah would not heare: therefore Iehoash King of Israel went vp: and he and Amaziah King of Iudah sawe one another in the face at Beth-shemesh which is in Iudah.
Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
12 And Iudah was put to the worse before Israel, and they fledde euery man to their tents.
Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
13 But Iehoash King of Israel tooke Amaziah King of Iudah, the sonne of Iehoash the sonne of Ahaziah, at Beth-shemesh, and came to Ierusalem, and brake downe the wall of Ierusalem from the gate of Ephraim to the corner gate, foure hundreth cubites.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
14 And he tooke all the gold and siluer, and all the vessels that were found in the house of the Lord, and in the treasures of the Kings house, and the children that were in hostage, and returned to Samaria.
Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
15 Concerning the rest of the acts of Iehoash which he did and his valiant deedes, and how he fought with Amaziah King of Iudah, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 And Iehoash slept with his fathers, and was buried at Samaria among the Kings of Israel: and Ieroboam his sonne reigned in his stead.
Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
17 And Amaziah the sonne of Ioash King of Iudah, liued after the death of Iehoash sonne of Iehoahaz King of Israel fifteene yeere.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
18 Concerning the rest of the actes of Amaziah, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
19 But they wrought treason against him in Ierusalem, and he fled to Lachish, but they sent after him to Lachish, and slewe him there.
Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
20 And they brought him on horses, and he was buried at Ierusalem with his fathers in the citie of Dauid.
Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
21 Then all the people of Iudah tooke Azariah which was sixteene yeere olde, and made him King for his father Amaziah.
Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
22 He built Elath, and restored it to Iudah, after that the King slept with his fathers.
Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
23 In the fifteenth yeere of Amaziah the sonne of Ioash King of Iudah, was Ieroboam the sonne of Ioash made King ouer Israel in Samaria, and reigned one and fourtie yeere.
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
24 And he did euill in the sight of the Lord: for he departed not from all the sinnes of Ieroboam the sonne of Nebat, which made Israel to sinne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
25 He restored the coast of Israel, from the entring of Hamath, vnto the Sea of the wildernesse, according to the worde of the Lord God of Israel, which he spake by his seruant Ionah the sonne of Amittai the Prophet, which was of Gath Hepher.
Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
26 For the Lord saw the exceeding bitter affliction of Israel, so that there was none shutte vp, nor any left, neyther yet any that could helpe Israel.
Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
27 Yet the Lord had not decreed to put out the name of Israel from vnder the heauen: therefore he preserued them by the hand of Ieroboam the sonne of Ioash.
Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
28 Concerning the rest of the actes of Ieroboam, and all that he did, and his valiant deedes, and how he fought, and how he restored Damascus, and Hamath to Iudah in Israel, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
29 So Ieroboam slept with his fathers, euen with the Kings of Israel, and Zachariah his sonne reigned in his steade.
Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.

< 2 Kings 14 >