< 2 Kings 12 >

1 In the seuenth yere of Iehu Iehoash began to reigne, and reigned fourty yeres in Ierusalem, and his mothers name was Zibiah of Beer-sheba.
A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
2 And Iehoash did that which was good in the sight of the Lord all his time that Iehoiada the Priest taught him.
Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
3 But the hie places were not taken away: for the people offred yet and burnt incense in the hie places.
Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
4 And Iehoash sayde to the Priestes, All the siluer of dedicate things that bee brought to the house of the Lord, that is, the money of them that are vnder the count, the money that euery man is set at, and all the money that one offereth willingly, and bringeth into the house of the Lord,
Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
5 Let the Priestes take it to them, euery man of his acquaintance: and they shall repaire the broken places of the house, wheresoeuer any decay is founde.
Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
6 Yet in the three and twentieth yeere of King Iehoash the Priestes had not mended that which was decayed in the Temple.
Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
7 Then King Iehoash called for Iehoiada the Priest, and the other Priestes, and sayd vnto them, Why repaire yee not the ruines of the Temple? nowe therefore receiue no more money of your acquaintance, except yee deliuer it to repaire the ruines of the Temple.
Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
8 So the Priestes consented to receiue no more money of the people, neither to repaire the decayed places of the Temple.
Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
9 Then Iehoiada the Priest tooke a chest and bored an hole in the lid of it, and set it beside the altar, on the right side, as euery man commeth into the Temple of the Lord. And the Priestes that kept the doore, put therein all the money that was brought into the house of the Lord.
Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
10 And when they sawe there was much money in the chest, the Kinges Secretarie came vp and the hie Priest, and put it vp after that they had tolde the money that was found in the house of the Lord,
Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
11 And they gaue the money made readie into the handes of them, that vndertooke the worke, and that had the ouersight of the house of the Lord; and they payed it out to the carpenters and builders that wrought vpon the house of the Lord,
Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
12 And to the masons and hewers of stone, and to bye timber and hewed stone, to repayre that was decayed in the house of the Lord, and for all that which was layed out for the reparation of the Temple.
masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
13 Howbeit there was not made for the house of the Lord bowles of siluer, instruments of musicke, basons, trumpets, nor any vessels of golde, or vessels of siluer of the money that was brought into the house of the Lord.
Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
14 But they gaue it to the workemen, which repayred therewith the house of the Lord.
an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
15 Moreouer, they reckoned not with the men, into whose handes they deliuered that money to be bestowed on workemen: for they dealt faithfully.
Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
16 The money of the trespasse offring and the money of ye sinne offrings was not brought into the house of the Lord: for it was the Priests.
Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
17 Then came vp Hazael King of Aram, and fought against Gath and tooke it, and Hazael set his face to goe vp to Ierusalem.
A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
18 And Iehoash King of Iudah tooke all the halowed thinges that Iehoshaphat, and Iehoram, and Ahaziah his fathers Kings of Iudah had dedicated, and that he himselfe had dedicated, and all the golde that was found in the treasures of the house of the Lord and in the Kings house, and sent it to Hazael King of Aram, and he departed from Ierusalem.
Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
19 Concerning the rest of the acts of Ioash and all that he did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 And his seruants arose and wrought treason, and slewe Ioash in the house of Millo, when he came downe to Silla:
Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
21 Euen Iozachar the sonne of Shimeath, and Iehozabad the sonne of Shomer his seruants smote him, and he dyed: and they buried him with his fathers in the citie of Dauid. And Amaziah his sonne reigned in his stead.
Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Kings 12 >