< 2 Kings 10 >

1 Ahab had nowe seuentie sonnes in Samaria. And Iehu wrote letters, and sent to Samaria vnto the rulers of Izreel, and to the Elders, and to the bringers vp of Ahabs children, to this effect,
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 Nowe when this letter commeth to you, (for ye haue with you your masters sonnes, yee haue with you both charets and horses, and a defenced citie, and armour)
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 Consider therefore which of your masters sonnes is best and most meete, and set him on his fathers throne, and fight for your masters house.
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 But they were exceedingly afraid, and saide, Behold two Kings coulde not stande before him, how shall we then stand?
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 And he that was gouernour of Ahabs house, and he that ruled the citie, and the Elders, and the bringers vp of the children sent to Iehu, saying, We are thy seruants, and will doe all that thou shalt bid vs: we will make no King: do what seemeth good to thee.
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Then he wrote another letter to them, saying, If ye be mine, and wil obey my voyce, take the heads of ye men that are your masters sonnes, and come to me to Izreel by to morowe this time. (Nowe the Kings sonnes, euen seuentie persons were with the great men of the citie, which brought them vp)
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 And when the letter came to them, they tooke the Kings sonnes, and slewe the seuentie persons, and layde their heads in baskets, and sent them vnto him to Izreel.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Then there came a messenger and tolde him, saying, They haue brought the heads of the Kings sonnes. And he sayd, Let them lay them on two heapes at the entring in of the gate vntil the morning.
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 And when it was day, he went out, and stood and sayd to all the people, Ye be righteous: behold, I conspired against my master, and slew him: but who slew all these?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Knowe nowe that there shall fall vnto the earth nothing of the word of the Lord, which the Lord spake concerning the house of Ahab: for the Lord hath brought to passe the things that hee spake by his seruant Eliiah.
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 So Iehu slew al that remained of the house of Ahab in Izreel, and all that were great with him, and his familiars and his priestes, so that he let none of his remaine.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 And he arose, and departed and came to Samaria. And as Iehu was in the way by an house where the shepheards did shere,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 He met with the brethre of Ahaziah king of Iudah, and sayd, Who are ye? And they answered, We are the brethren of Ahaziah, and goe downe to salute the children of the King and the children of the Queene.
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 And he sayde, Take them aliue. And they tooke them aliue, and slew them at the well beside the house where the sheepe are shorne, euen two and fourtie men, and he left not one of them.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 And when he was departed thence, hee met with Iehonadab the sonne of Rechab comming to meete him, and he blessed him, and sayde to him, Is thine heart vpright, as mine heart is towarde thine? And Iehonadab answered, Yea, doubtlesse. Then giue me thine hande. And when he had giuen him his hande, he tooke him vp to him into the charet.
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 And he sayde, Come with me, and see the zeale that I haue for the Lord: so they made him ride in his charet.
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 And when he came to Samaria, he slew all that remained vnto Ahab in Samaria, till he had destroyed him, according to the worde of the Lord, which he spake to Eliiah.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Then Iehu assembled all the people, and sayd vnto them, Ahab serued Baal a litle, but Iehu shall serue him much more.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Now therefore call vnto me all ye prophets of Baal, all his seruants, and all his priests, and let not a man be lacking: for I haue a great sacrifice for Baal: whosoeuer is lacking, he shall not liue. But Iehu did it by a subtiltie to destroy ye seruats of Baal.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 And Iehu sayd, Proclaime a solemne assemblie for Baal. And they proclaimed it.
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 So Iehu sent vnto all Israel, and all the seruants of Baal came, and there was not a man left that came not. And they came into the house of Baal, and the house of Baal was full from ende to ende.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Then he said vnto him that had the charge of the vestrie, Bring forth vestments for al the seruants of Baal. And he brought the out vestments.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 And when Iehu went, and Iehonadab the sonne of Rechab into the house of Baal, he sayde vnto the seruants of Baal, Searche diligently, and looke, lest there be here with you any of the seruants of the Lord, but the seruants of Baal only.
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 And when they went in to make sacrifice and burnt offering, Iehu appoynted foure score men without, and sayd, If any of the men whome I haue brought into your hands, escape, his soule shalbe for his soule.
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 And when hee had made an ende of the burnt offring, Iehu sayde to the garde, and to the captaines, Goe in, slay them, let not a man come out. And they smote them with the edge of the sworde. And the garde, and the captaines cast them out, and went vnto the citie, where was the temple of Baal.
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 And they brought out the images of the temple of Baal, and burnt them.
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 And they destroyed the image of Baal, and threwe downe the house of Baal, and made a iakes of it vnto this day.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 So Iehu destroyed Baal out of Israel.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 But from the sinnes of Ieroboam the sonne of Nebat which made Israel to sinne, Iehu departed not from them, neither from the golden calues that were in Beth-el and that were in Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 And the Lord sayde vnto Iehu, Because thou hast diligently executed that which was right in mine eyes, and hast done vnto the house of Ahab according to all things that were in mine heart, therefore shall thy sonnes vnto the fourth generation sit on the throne of Israel.
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 But Iehu regarded not to walke in the law of the Lord God of Israel with all his heart: for hee departed not from the sinnes of Ieroboam, which made Israel to sinne.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 In those dayes the Lord began to lothe Israel, and Hazael smote them in all the coastes of Israel,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 From Iorden Eastward, euen all the land of Gilead, the Gadites, and the Reubenites, and them that were of Manasseh, from Aroer (which is by the riuer Arnon) and Gilead and Bashan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Concerning the rest of the actes of Iehu, and all that he did, and all his valiant deedes, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 And Iehu slept with his fathers, and they buryed him in Samaria, and Iehoahaz his sonne reigned in his stead.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 And the time that Iehu reigned ouer Israel in Samaria is eight and twentie yeeres.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 2 Kings 10 >