< 2 Chronicles 19 >

1 And Iehoshaphat the King of Iudah returned safe to his house in Ierusalem.
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 And Iehu the sonne of Hanani the Seer went out to meete him, and said to King Iehoshaphat, Wouldest thou helpe the wicked, and loue them that hate the Lord? therefore for this thing the wrath of the Lord is vpon thee.
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 Neuertheles good things are found in thee, because thou hast taken away ye groues out of the land, and hast prepared thine heart to seeke God.
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 So Iehoshaphat dwelt at Ierusalem, and returned and went through the people from Beer-sheba to mount Ephraim, and brought them againe vnto the Lord God of their fathers.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 And hee set iudges in the lande throughout all the strong cities of Iudah, citie by citie,
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 And said to the iudges, Take heede what ye doe: for yee execute not the iudgements of man, but of the Lord, and he will be with you in the cause and iudgement.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 Wherefore nowe let the feare of the Lord be vpon you: take heede, and do it: for there is no iniquitie with the Lord our God, neither respect of persons, nor receiuing of reward.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 Moreouer in Ierusalem did Iehoshaphat set of the Leuites, and of the Priests and of the chiefe of the families of Israel, for the iudgement and cause of the Lord: and they returned to Ierusale.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 And he charged them, saying, Thus shall yee doe in the feare of the Lord faithfully and with a perfite heart.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 And in euery cause that shall come to you of your brethren that dwel in their cities, betweene blood and blood, betweene law and precept, statutes and iudgements, ye shall iudge them, and admonish them that they trespasse not against the Lord, that wrath come not vpon you and vpon your brethren. This shall ye do and trespasse not.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 And behold, Amariah the Priest shalbe the chiefe ouer you in all matters of the Lord, and Zebadiah ye sonne of Ishmael, a ruler of the house of Iudah, shalbe for al the Kings affaires, and the Leuites shalbe officers before you. Bee of courage, and doe it, and the Lord shalbe with the good.
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Chronicles 19 >