< 2 Chronicles 17 >

1 And Iehosphat his sonne reigned in his steade, and preuailed against Israel.
Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki ya kuma kahu sosai gāba da Isra’ila.
2 And he put garisons in all the strong cities of Iudah, and set bandes in the lande of Iudah and in the cities of Ephraim, which Asa his father had taken.
Ya kafa mayaƙa a dukan biranen katangar Yahuda, ya kuma sa runduna a Yahuda da kuma a garuruwan Efraim da mahaifinsa Asa ya ci da yaƙi.
3 And the Lord was with Iehoshaphat, because he walked in the first wayes of his father Dauid, and sought not Baalim,
Ubangiji kuwa yana tare da Yehoshafat domin a shekarunsa na farko-farko ya yi tafiya a hanyoyin da kakansa Dawuda ya bi. Bai nemi shawarar Ba’al ba
4 But sought the Lord God of his father, and walked in his commandements, and not after the trade of Israel.
amma ya nemi Allah na kakansa ya kuma bi umarnansa a maimakon ayyukan da Isra’ila ke yi.
5 Therefore the Lord stablished the kingdome in his hande, and all Iudah brought presents to Iehoshaphat, so that he had of riches and honour in abundance.
Ubangiji ya kafa mulkin a ƙarƙashin ikonsa; dukan Yahuda kuwa suka kawo kyautai wa Yehoshafat, ta haka ya yi arziki sosai da kuma girma.
6 And he lift vp his heart vnto the wayes of the Lord, and he tooke away moreouer the hie places and the groues out of Iudah.
Zuciyarsa ta duƙufa ga hanyoyin Ubangiji, bugu da ƙari, ya kawar masujadan kan tudu da ginshiƙan Ashera daga Yahuda.
7 And in the thirde yere of his reigne he sent his princes, Ben-hail, and Obadiah, and Zechariah, and Nethaneel, and Michaiah, that they should teach in the cities of Iudah,
A shekara ta uku ta mulkinsa, ya aiki ma’aikatansa Ben-Hayil, Obadiya, Zakariya, Netanel da Mikahiya su yi koyarwa a garuruwan Yahuda.
8 And with them Leuites, Shemaiah, and Nethaniah, and Zebadiah, and Asahel, and Shemiramoth, and Iehonathan, and Adoniiah, and Tobiiah, and Tob-adoniiah, Leuites, and with the Elishama and Iehoram Priestes.
Tare da su akwai waɗansu Lawiyawa, Shemahiya, Netaniya, Zebadiya, Asahel, Shemiramot, Yehonatan, Adoniya, Tobiya da Tob Adoniya, da kuma firistoci Elishama da Yehoram.
9 And they taught in Iudah, and had the booke of the Lawe of the Lord with them, and went about throughout all the cities of Iudah, and taught the people.
Suka yi koyarwa a dukan Yahuda, suna ɗauke da Littafin Dokar Ubangiji tare da su; suka tafi ko’ina a dukan garuruwan Yahuda suka koyar da mutane.
10 And the feare of the Lord fell vpon all the kingdomes of ye lands that were round about Iudah, and they fought not against Iehoshaphat.
Tsoron Ubangiji ya kama dukan masarautun ƙasashen da suke kewaye da Yahuda, har ba su yi yaƙi da Yehoshafat ba.
11 Also some of the Philistims brought Iehoshaphat giftes and tribute siluer, and the Arabians brought him flockes, seuen thousande and seuen hundreth rammes, and seuen thousande and seuen hundreth hee goates.
Waɗansu Filistiyawa suka kawo wa Yehoshafat kyautai da azurfa a matsayin haraji, Larabawa kuwa suka kawo masa garkuna, raguna dubu bakwai da ɗari bakwai da kuma awaki dubu bakwai da ɗari bakwai.
12 So Iehoshaphat prospered and grewe vp on hie: and he built in Iudah palaces and cities of store.
Yehoshafat ya yi ta ƙaruwa a ƙarfi; ya gina katanga da biranen ajiya a Yahuda
13 And he had great workes in the cities of Iudah, and men of warre, and valiant men in Ierusalem.
da kuma tanade-tanade masu yawa a garuruwan Yahuda. Ya kuma ajiye gogaggu mayaƙa a Urushalima.
14 And these are the nombers of them after the house of their fathers, In Iudah were captaines of thousands, Adnah the captaine, and with him of valiant men three hundreth thousande.
Ɗaukar da aka yi musu bisa ga iyalai yana kamar haka. Daga Yahuda, shugaban ƙungiya 1,000. Adna ne shugaba, tare da jarumawa 300,000;
15 And at his hande Iehohanan a captaine, and with him two hundreth and fourescore thousande.
biye da shi, Yehohanan shi ne shugaba, yana da sojoji 280,000;
16 And at his hande Amasiah the sonne of Zichri, which willingly offered him selfe vnto the Lord, and with him two hundreth thousand valiant men.
biye da shi, Amasiya ɗan Zikri, wanda ya ba da kansa da yardar rai don hidimar Ubangiji, yana da sojoji 200,000.
17 And of Beniamin, Eliada a valiant man, and with him armed men with bowe and shielde two hundreth thousand.
Daga Benyamin, Eliyada, jarumi soja, yana da sojoji 200,000 riƙe da baka da garkuwoyi;
18 And at his hand Iehozabad, and with him an hundreth and fourescore thousand armed to the warre.
biye da shi, Yehozabad, yana da sojoji 18,000 shiryayyu don yaƙi.
19 These waited on the King, besides those which the King put in the strong cities thoroughout all Iudah.
Waɗannan su ne suka yi wa sarki hidima, ban da waɗanda aka sa a biranen katanga ko’ina a Yahuda.

< 2 Chronicles 17 >