< 1 Samuel 4 >

1 And Samuel spake vnto all Israel: and Israel went out against the Philistims to battel and pitched beside Eben-ezer: and the Philistims pitched in Aphek.
Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
2 And the Philistims put themselues in aray against Israel: and when they ioyned the battell, Israel was smitten downe before the Philistims: who slewe of the armie in the fielde about foure thousand men.
Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
3 So when the people were come into the campe, the Elders of Israel said, Wherefore hath the Lord smitten vs this day before ye Philistims? let vs bring the Arke of the couenant of the Lord out of Shiloh vnto vs, that when it commeth among vs, it may saue vs out of the hande of our enemies.
Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
4 Then the people sent to Shiloh, and brought from thence the Arke of the couenant of the Lord of hostes, who dwelleth betweene the Cherubims: and there were the two sonnes of Eli, Hophni, and Phinehas, with the Arke of the couenant of God.
Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
5 And when the Arke of the couenant of the Lord came into the hoste, all Israel shouted a mightie shoute, so that the earth rang againe.
Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
6 And when the Philistims heard the noyse of the shoute, they said, What meaneth the sound of this mightie shoute in the host of the Ebrewes? and they vnderstoode, that the Arke of the Lord was come into the hoste.
Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
7 And the Philistims were afraide, and saide, God is come into the hoste: therefore saide they, Wo vnto vs: for it hath not bene so heretofore.
sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
8 Wo vnto vs, who shall deliuer vs out of the hande of these mightie Gods? these are the Gods that smote the Egyptians with all the plagues in the wildernes.
Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
9 Be strong and play the men, O Philistims, that ye be not seruants vnto the Ebrewes, as they haue serued you: be valiant therefore, and fight.
Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
10 And the Philistims fought, and Israel was smitten downe, and fled euery man into his tent: and there was an exceeding great slaughter: for there fell of Israel thirtie thousand footemen.
Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
11 And the Arke of God was taken, and the two sonnes of Eli, Hophni and Phinehas died.
Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
12 And there ranne a man of Beniamin out of the armie, and came to Shiloh the same day with his clothes rent, and earth vpon his head.
A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
13 And when hee came, loe, Eli sate vpon a seate by the wayside, wayting: for his heart feared for the Arke of God and when the man came into the citie to tell it, all the citie cried out.
Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
14 And when Eli heard the noyse of the crying, he sayd, What meaneth this noyse of the tumult? and the man came in hastily, and tolde Eli.
Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
15 (Nowe Eli was fourescore and eighteene yeere olde, and his eyes were dimme that hee could not see)
wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
16 And the man sayd vnto Eli, I came from the armie, and I fled this day out of the hoste: and he sayd, What thing is done, my sonne?
Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
17 Then the messenger answered and sayd, Israel is fled before the Philistims, and there hath bene also a great slaughter among the people: and moreouer thy two sonnes, Hophni and Phinehas are dead, and the Arke of God is taken.
Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
18 And when he had made mention of the Arke of God, Eli fell from his seate backward by the side of the gate, and his necke was broken, and he dyed: for he was an olde man and heauie: and he had iudged Israel fourtie yeeres.
Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
19 And his daughter in lawe Phinehas wife was with childe neere her trauell: and when she heard the report that the Arke of God was taken, and that her father in lawe and her husband were dead, she bowed her selfe, and trauailed: for her paines came vpon her.
Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
20 And about the time of her death, the women that stoode about her, sayd vnto her, Feare not: for thou hast borne a sonne: but she answered not, nor regarded it.
Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
21 And she named the childe Ichabod, saying, The glory is departed from Israel, because the Arke of God was taken, and because of her father in lawe and her husband.
Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
22 She sayde againe, The glory is departed from Israel: for the Arke of God is taken.
Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”

< 1 Samuel 4 >