< 1 Samuel 20 >

1 And Dauid fled from Naioth in Ramah, and came and sayd before Ionathan, What haue I done? what is mine iniquitie? and what sinne haue I committed before thy father, that he seeketh my life?
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 And he sayde vnto him, God forbid, thou shalt not die: beholde, my father will do nothing great nor small, but he will shewe it me: and why should my father hide this thing from me? he will not doe it.
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 And Dauid sware againe and sayd, Thy father knoweth that I haue found grace in thine eyes: therefore he thinketh, Ionathan shall not knowe it, lest he be sorie: but in deede, as the Lord liueth, and as thy soule liueth, there is but a step betweene me and death.
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 Then said Ionathan vnto Dauid, Whatsoeuer thy soule requireth, that I wil do vnto thee.
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 And Dauid said vnto Ionathan, Behold, to morowe is the first day of the moneth, and I shoulde sit with the King at meate: but let me goe, that I may hide my selfe in the fieldes vnto the third day at euen.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 If thy father make mention of me, then say, Dauid asked leaue of me, that he might goe to Beth-lehem to his owne citie: for there is a yeerely sacrifice for all that familie.
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 And if he say thus, It is well, thy seruant shall haue peace: but if he be angrie, be sure that wickednesse is concluded of him.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 So shalt thou shew mercy vnto thy seruant: for thou hast ioyned thy seruant into a couenant of the Lord with thee, and if there be in me iniquitie, slay thou me: for why shouldest thou bring me to thy father?
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 And Ionathan answered, God keepe that from thee: for if I knewe that wickednesse were concluded of my father to come vpon thee, would not I tell it thee?
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 Then said Dauid to Ionathan, Who shall tell me? how shall I knowe, if thy father answere thee cruelly?
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 And Ionathan sayde to Dauid, Come and let vs goe out into the fielde: and they twaine went out into the fielde.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 Then Ionathan sayde to Dauid, O Lord God of Israel, when I haue groped my fathers minde to morow at this time, or within this three dayes, and if it be well with Dauid, and I then send not vnto thee, and shewe it thee,
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 The Lord doe so and much more vnto Ionathan: but if my father haue minde to doe thee euill, I will shew thee also, and sende thee away, that thou mayest goe in peace: and the Lord be with thee as he hath bene with my father.
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 Likewise I require not whiles I liue: for I dout not but thou wilt shew me the mercy of the Lord, that I die not.
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 But I require that thou cut not off thy mercie from mine house for euer: no, not when the Lord hath destroyed the enemies of Dauid, euery one from the earth.
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 So Ionathan made a bond with the house of Dauid, saying, Let the Lord require it at the hands of Dauids enemies.
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 And againe Ionathan sware vnto Dauid, because he loued him (for he loued him as his owne soule)
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 Then said Ionathan to him, To morowe is the first day of the moneth: and thou shalt be looked for, for thy place shalbe emptie.
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 Therefore thou shalt hide thy selfe three dayes, then thou shalt goe downe quickely and come to the place where thou diddest hide thy selfe, when this matter was in hand, and shalt remayne by the stone Ezel.
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 And I will shoote three arrowes on the side thereof, as though I shot at a marke.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 And after I wil sende a boy, saying, Goe, seeke the arrowes. If I say vnto the boy, See, the arrowes are on this side thee, bring them, and come thou: for it is well with thee and no hurt, as the Lord liueth.
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 But if I say thus vnto the boy, Behold, the arrowes are beyonde thee, goe thy way: for the Lord hath sent thee away.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 As touching the thing which thou and I haue spoken of, beholde, the Lord be betweene thee and me for euer.
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 So Dauid hid him selfe in the field: and when the first day of the moneth came, the King sate to eate meate.
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 And the King sate, as at other times vpon his seate, euen vpon his seate by the wall: and Ionathan arose, and Abner sate by Sauls side, but Dauids place was emptie.
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 And Saul sayde nothing that day: for hee thought, Some thing hath befallen him, though he were cleane, or els becaus he was not purified.
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 But on the morowe which was the second day of the moneth, Dauids place was emptie againe: and Saul sayde vnto Ionathan his sonne, Wherefore commeth not the sonne of Ishai to meate, neither yesterday nor to day?
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 And Ionathan answered vnto Saul, Dauid required of me, that he might goe to Beth-lehem.
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 For he sayde, Let me goe, I pray thee: for our familie offreth a sacrifice in the citie, and my brother hath sent for me: therfore now if I haue found fauour in thine eyes, let me goe, I pray thee, and see my brethren: this is the cause that he commeth not vnto the Kings table.
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 Then was Saul angrie with Ionathan, and sayde vnto him, Thou sonne of the wicked rebellious woman, doe not I know, that thou hast chosen the sonne of Ishai to thy confusion, and to the confusion and shame of thy mother?
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 For as long as the sonne of Ishai liueth vpon the earth, thou shalt not be stablished, nor thy kingdome: wherefore now send and fet him vnto me, for he shall surely die.
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 And Ionathan answered vnto Saul his father, and said vnto him, Wherefore shall he die? what hath he done?
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 And Saul cast a speare at him to hit him, whereby Ionathan knew, that it was determined of his father to slay Dauid.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 So Ionathan arose from the table in a great anger, and did eate no meate the seconde day of the moneth: for he was sorie for Dauid, and because his father had reuiled him.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 On the next morning therefore Ionathan than went out into the fielde, at the time appoynted with Dauid, and a litle boy with him.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 And he saide vnto his boy, Runne now, seeke the arrowes which I shoote, and as the boy ran, he shot an arrowe beyond him.
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 And when the boy was come to the place where the arrowe was that Ionathan had shot, Ionathan cryed after the boy, and sayde, Is not the arrowe beyond thee?
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 And Ionathan cryed after the boy, Make speede, haste and stand not still: and Ionathans boy gathered vp the arrowes, and came to his master,
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 But the boy knewe nothing: onely Ionathan and Dauid knew the matter.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 Then Ionathan gaue his bowe and arrowes vnto the boy that was with him, and sayd vnto him, Goe, carrie them into the citie.
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 Assoone as the boy was gone, Dauid arose out of a place that was towarde the South, and fel on his face to the ground, and bowed him selfe three times: and they kissed one another, and wept both twaine, till Dauid exceeded.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 Therefore Ionathan said to Dauid, Goe in peace: that which we haue sworne both of vs in the Name of the Lord, saying, The Lord be betweene me and thee, and betweene my seede and betweene thy seede, let it stand for euer. And he arose and departed, and Ionathan went into the citie.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >