< 1 Kings 15 >

1 And in the eighteenth yeere of King Ieroboam the sonne of Nebat, reigned Abiiam ouer Iudah.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 Three yeere reigned hee in Ierusalem, and his mothers name was Maachah the daughter of Abishalom.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 And hee walked in all the sinnes of his father, which hee had done before him: and his heart was not perfit with the Lord his God as the heart of Dauid his father.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 But for Dauids sake did the Lord his God giue him a light in Ierusalem, and set vp his sonne after him, and established Ierusalem,
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 Because Dauid did that which was right in the sight of the Lord, and turned from nothing that he commanded him, all the dayes of his life, saue onely in the matter of Vriah the Hittite.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 And there was warre betweene Rehoboam and Ieroboam as long as he liued.
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 The rest also of the actes of Abiiam, and all that he did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah? there was also warre betweene Abiiam, and Ieroboam.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 And Abiiam slept with his fathers, and they buried him in the citie of Dauid: and Asa his sonne reigned in his steade.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 And in the twentie yeere of Ieroboam King of Israel reigned Asa ouer Iudah.
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 He reigned in Ierusalem one and fourtie yeere, and his mothers name was Maachah the daughter of Abishalom.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 And Asa did right in the eyes of the Lord, as did Dauid his father.
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 And he tooke away the Sodomites out of the lande, and put away all the idoles that his fathers had made.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 And he put downe Maachah his mother also from her estate, because shee had made an idole in a groue: and Asa destroyed her idoles, and burnt them by the brooke Kidron.
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 But they put not downe the hie places. Neuertheles Asas heart was vpright with the Lord all his dayes.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 Also he brought in the holy vessels of his father, and the things that he had dedicated vnto ye house of the Lord, siluer, and golde, and vessels.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 And there was warre betweene Asa and Baasha King of Israel all their dayes.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 Then Baasha king of Israel went vp against Iudah, and buylt Ramah, so that he woulde let none go out or in to Asa King of Iudah.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 Then Asa tooke all the siluer and the gold that was left in the treasures of the house of the Lord, and the treasures of the kings house, and deliuered them into the handes of his seruantes, and King Asa sent them to Ben-hadad the sonne of Tabrimon, the sonne of Hezion king of Aram that dwelt at Damascus, saying,
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 There is a couenant betweene me and thee, and betweene my father and thy father: behold, I haue sent vnto thee a present of siluer and golde: come, breake thy couenant with Baasha King of Israel, that he may depart from me.
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 So Ben-hadad hearkened vnto King Asa, and sent the captaines of the hosts, which he had, against the cities of Israel, and smote lion, and Dan, and Abel-beth-maachah, and all Cinneroth, with all the land of Naphtali.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 And when Baasha heard thereof, hee left buylding of Ramah, and dwelt in Tirzah.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Then king Asa assembled al Iudah, none excepted. and they tooke the stones of Ramah, and the timber thereof, wherewith Baasha had buylt, and King Asa built with them Geba of Beniamin and Mizpah.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 And the rest of all the actes of Asa, and all his might, and all that he did, and the cities which he buylt, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah? but in his olde age he was diseased in his feete.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 And Asa slept with his fathers, and was buried with his fathers in the citie of Dauid his father. And Iehoshaphat his sonne reigned in his steade.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 And Nadab the sonne of Ieroboam began to reigne ouer Israel the second yere of Asa King of Iudah, and reigned ouer Israel two yeere.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 And he did euill in the sight of the Lord, walking in the way of his father, and in his sinne wherewith he made Israel to sinne.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 And Baasha the sonne of Ahijah of ye house of Issachar conspired against him, and Baasha slue him at Gibbethon, which belonged to the Philistims: for Nadab and all Israel layde siege to Gibbethon.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 Euen in the third yeere of Asa King of Iudah did Baasha slay him, and reigned in his steade.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 And when he was King, he smote all the house of Ieroboam, he left none aliue to Ieroboam, vntill hee had destroyed him, according to the word of the Lord which he spake by his seruant Ahijah the Shilonite,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 Because of the sinnes of Ieroboam which he committed, and wherewith he made Israel to sinne, by his prouocation, wherewith he prouoked the Lord God of Israel.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 And the residue of the actes of Nadab, and all that he did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 And there was warre betweene Asa and Baasha King of Israel, all their dayes.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 In the thirde yeere of Asa King of Iudah, began Baasha the sonne of Ahijah to reigne ouer all Israel in Tirzah, and reigned foure and twentie yeeres.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 And he did euill in the sight of the Lord, walking in the way of Ieroboam, and in his sinne, wherewith he made Israel to sinne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.

< 1 Kings 15 >