< Amos 1 >

1 Here is the message that was given to Amos, a shepherd from Tekoa in Judah. This is what he saw concerning Israel when Uzziah was king of Judah and Jeroboam, son of Jehoash, was king of Israel, two years before the earthquake.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 And he said, The Lord roars from Zion, he shouts from Jerusalem. The shepherds' pastures wither, the top of Mount Carmel dries up.
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 This is what the Lord says: The people of Damascus have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, for they beat the people of Gilead with sharp iron threshing tools.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 So I will send fire down on the house of Hazael and burn up Ben-Hadad's fortresses.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 I will smash the gates of Damascus, I will cut down those who live in the Valley of Aven, and the ruler from Beth Eden. The people of Aram will be deported as prisoners to the land of Kir, says the Lord.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 This is what the Lord says: The people of Gaza have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, for they sent into exile whole communities, handing them over to Edom.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 So I will send down fire on the walls of Gaza and burn up its fortresses.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 I will cut down those who live in Ashdod and the ruler of Ashkelon. I will turn to punish Ekron and the Philistines who remain will die, says the Lord God.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 This is what the Lord says: The people of Tyre have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, for they exiled whole communities, handing them over to Edom, and did not keep their agreement to help each other as members of the same family.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 So I will send down fire on the walls of Tyre and burn up its fortresses.
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 This is what the Lord says: The people of Edom have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, for they hunted down the Israelites to whom they were related, killing them with swords. They attacked without mercy, tearing the Israelites to pieces in an angry rage that never stopped.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 So I will send down fire on Teman, and I will burn up the fortresses of Bozrah.
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 This is what the Lord says: The people of Ammon have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, because they ripped open pregnant women in Gilead as part of their war to enlarge their territory.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 I will set fire to the walls of Rabbah and burn up its fortresses. There will be shouts on the day of battle which will whirl with rage like a windstorm.
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 Their king will be sent into exile together with his princes, says the Lord.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< Amos 1 >