< Amos 2 >

1 This is what the Lord says: The people of Moab have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, because they desecrated the bones of the king of Edom by burning them, turning them into lime.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
2 So I will send down fire on Moab, and I will burn up the fortresses of Kerioth, and the people of Moab will die in the midst of uproar, battle cries, and the sound of the trumpet.
Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
3 I will cut down their king and all their princes with him, says the Lord.
Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
4 This is what the Lord says: The people of Judah have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, because they rejected the law of the Lord and have not kept his commands. Their lies have led them astray, the same lies that their forefathers followed.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
5 So I will send down fire on Judah, and I will burn up the fortresses of Jerusalem.
Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
6 This is what the Lord says: The people of Israel have repeatedly sinned and so I will not hesitate to punish them, because they sell good people for silver, and poor people for a pair of sandals.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
7 They trample the heads of the poor into the dust, and push the needy out of the way. A man and his father have sex with the same servant girl so that my holy name is profaned.
Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
8 At every altar they stretch themselves out in clothes taken from debtors as collateral, in the temple of their god they drink wine taken from the people they fined.
Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
9 Yet it was I was the one who destroyed the Amorites before you, even though they were as tall as cedars and as strong as oaks. I destroyed them root and branch.
“Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
10 It was I who brought you out of the land of Egypt and led you through the desert for forty years so that you could take the Amorites' land.
Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
11 I appointed some of your sons to be prophets, and some of your young men to be Nazirites. Isn't this true, people of Israel?
“Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
12 But you made the Nazirites sin by drinking wine, and you told the prophets, “Don't tell us what God says.”
“Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
13 Now see what I am going to do. I will crush you where you are, as if crushed by a heavy cart loaded down with sheaves of grain.
“Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
14 Not even your fastest runners will escape; strong men will lose their strength. Even the greatest warrior will not be able to save his life.
Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
15 The archer will not stand his ground. The quickest on his feet will not be able to get away, and even those on horseback will not save themselves.
’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
16 On that day even the bravest of the mighty warriors will run away naked, says the Lord.
Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.

< Amos 2 >