< Luke 24 >

1 But on the morrow of the sabbath, very early indeed in the morning, they came to the tomb, bringing the aromatic spices which they had prepared.
Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
2 And they found the stone rolled away from the sepulchre.
Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
3 And when they had entered they found not the body of the Lord Jesus.
Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
4 And it came to pass as they were in perplexity about it, that behold, two men suddenly stood by them in shining raiment.
Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
5 And as they were filled with fear and bowed their faces to the ground, they said to them, Why seek ye the living one among the dead?
A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
6 He is not here, but is risen: remember how he spoke to you, being yet in Galilee,
Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
7 saying, The Son of man must be delivered up into the hands of sinners, and be crucified, and rise the third day.
‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
8 And they remembered his words;
Sai suka tuna da maganarsa.
9 and, returning from the sepulchre, related all these things to the eleven and to all the rest.
Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
10 Now it was Mary of Magdala, and Johanna, and Mary the [mother] of James, and the others with them, who told these things to the apostles.
Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
11 And their words appeared in their eyes as an idle tale, and they disbelieved them.
Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
12 But Peter, rising up, ran to the sepulchre, and stooping down he sees the linen clothes lying there alone, and went away home, wondering at what had happened.
Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
13 And behold, two of them were going on the same day to a village distant sixty stadia from Jerusalem, called Emmaus;
A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
14 and they conversed with one another about all these things which had taken place.
Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
15 And it came to pass as they conversed and reasoned, that Jesus himself drawing nigh, went with them;
Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
16 but their eyes were holden so as not to know him.
Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
17 And he said to them, What discourses are these which pass between you as ye walk, and are downcast?
Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
18 And one [of them], named Cleopas, answering said to him, Thou sojournest alone in Jerusalem, and dost not know what has taken place in it in these days?
Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
19 And he said to them, What things? And they said to him, The things concerning Jesus the Nazaraean, who was a prophet mighty in deed and word before God and all the people;
Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
20 and how the chief priests and our rulers delivered him up to [the] judgment of death and crucified him.
Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
21 But we had hoped that he was [the one] who is about to redeem Israel. But then, besides all these things, it is now, to-day, the third day since these things took place.
Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
22 And withal, certain women from amongst us astonished us, having been very early at the sepulchre,
Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
23 and, not having found his body, came, saying that they also had seen a vision of angels, who say that he is living.
amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
24 And some of those with us went to the sepulchre, and found it so, as the women also had said, but him they saw not.
Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
25 And he said to them, O senseless and slow of heart to believe in all that the prophets have spoken!
Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
26 Ought not the Christ to have suffered these things and to enter into his glory?
Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
27 And having begun from Moses and from all the prophets, he interpreted to them in all the scriptures the things concerning himself.
Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
28 And they drew near to the village where they were going, and he made as though he would go farther.
Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
29 And they constrained him, saying, Stay with us, for it is toward evening and the day is declining. And he entered in to stay with them.
Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
30 And it came to pass as he was at table with them, having taken the bread, he blessed, and having broken it, gave it to them.
Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
31 And their eyes were opened, and they recognised him. And he disappeared from them.
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
32 And they said to one another, Was not our heart burning in us as he spoke to us on the way, [and] as he opened the scriptures to us?
Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
33 And rising up the same hour, they returned to Jerusalem. And they found the eleven, and those with them, gathered together,
Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
34 saying, The Lord is indeed risen and has appeared to Simon.
suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
35 And they related what [had happened] on the way, and how he was made known to them in the breaking of bread.
Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
36 And as they were saying these things, he himself stood in their midst, and says to them, Peace [be] unto you.
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37 But they, being confounded and being frightened, supposed they beheld a spirit.
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38 And he said to them, Why are ye troubled? and why are thoughts rising in your hearts?
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39 behold my hands and my feet, that it is I myself. Handle me and see, for a spirit has not flesh and bones as ye see me having.
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40 And having said this he shewed them his hands and his feet.
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41 But while they yet did not believe for joy, and were wondering, he said to them, Have ye anything here to eat?
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42 And they gave him part of a broiled fish and of a honeycomb;
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43 and he took it and ate before them.
ya karɓa ya ci a gabansu.
44 And he said to them, These [are] the words which I spoke to you while I was yet with you, that all that is written concerning me in the law of Moses and prophets and psalms must be fulfilled.
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45 Then he opened their understanding to understand the scriptures,
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
46 and said to them, Thus it is written, and thus it behoved the Christ to suffer, and to rise from among the dead the third day;
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
47 and that repentance and remission of sins should be preached in his name to all the nations beginning at Jerusalem.
Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
48 And ye are witnesses of these things.
Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
49 And behold, I send the promise of my Father upon you; but do ye remain in the city till ye be clothed with power from on high.
Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
50 And he led them out as far as Bethany, and having lifted up his hands, he blessed them.
Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
51 And it came to pass as he was blessing them, he was separated from them and was carried up into heaven.
Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
52 And they, having done him homage, returned to Jerusalem with great joy,
Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
53 and were continually in the temple praising and blessing God.
Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.

< Luke 24 >