< John 1 >

1 In [the] beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 He was in the beginning with God.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 All things received being through him, and without him not one [thing] received being which has received being.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 In him was life, and the life was the light of men.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 And the light appears in darkness, and the darkness apprehended it not.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 There was a man sent from God, his name John.
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 He came for witness, that he might witness concerning the light, that all might believe through him.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 He was not the light, but that he might witness concerning the light.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 The true light was that which, coming into the world, lightens every man.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 He was in the world, and the world had [its] being through him, and the world knew him not.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 He came to his own, and his own received him not;
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 but as many as received him, to them gave he [the] right to be children of God, to those that believe on his name;
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 who have been born, not of blood, nor of flesh's will, nor of man's will, but of God.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 And the Word became flesh, and dwelt among us (and we have contemplated his glory, a glory as of an only-begotten with a father), full of grace and truth;
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 (John bears witness of him, and he has cried, saying, This was he of whom I said, He that comes after me is preferred before me, for he was before me; )
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 for of his fulness we all have received, and grace upon grace.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 For the law was given by Moses: grace and truth subsists through Jesus Christ.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 No one has seen God at any time; the only-begotten Son, who is in the bosom of the Father, he hath declared [him].
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 And this is the witness of John, when the Jews sent from Jerusalem priests and Levites that they might ask him, Thou, who art thou?
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 And he acknowledged and denied not, and acknowledged, I am not the Christ.
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 And they asked him, What then? Art thou Elias? And he says, I am not. Art thou the prophet? And he answered, No.
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 They said therefore to him, Who art thou? that we may give an answer to those who sent us. What sayest thou of thyself?
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 He said, I [am] [the] voice of one crying in the wilderness, Make straight the path of [the] Lord, as said Esaias the prophet.
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 And they were sent from among the Pharisees.
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 And they asked him and said to him, Why baptisest thou then, if thou art not the Christ, nor Elias, nor the prophet?
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 John answered them saying, I baptise with water. In the midst of you stands, whom ye do not know,
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 he who comes after me, the thong of whose sandal I am not worthy to unloose.
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 These things took place in Bethany, across the Jordan, where John was baptising.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 On the morrow he sees Jesus coming to him, and says, Behold the Lamb of God, who takes away the sin of the world.
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 He it is of whom I said, A man comes after me who takes a place before me, because he was before me;
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 and I knew him not; but that he might be manifested to Israel, therefore have I come baptising with water.
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 And John bore witness, saying, I beheld the Spirit descending as a dove from heaven, and it abode upon him.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 And I knew him not; but he who sent me to baptise with water, he said to me, Upon whom thou shalt see the Spirit descending and abiding on him, he it is who baptises with [the] Holy Spirit.
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 And I have seen and borne witness that this is the Son of God.
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Again, on the morrow, there stood John and two of his disciples.
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 And, looking at Jesus as he walked, he says, Behold the Lamb of God.
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 And the two disciples heard him speaking, and followed Jesus.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 But Jesus having turned, and seeing them following, says to them, What seek ye? And they said to him, Rabbi (which, being interpreted, signifies Teacher), where abidest thou?
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 He says to them, Come and see. They went therefore, and saw where he abode; and they abode with him that day. It was about the tenth hour.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 Andrew, the brother of Simon Peter, was one of the two who heard [this] from John and followed him.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 He first finds his own brother Simon, and says to him, We have found the Messias (which being interpreted is Christ).
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 And he led him to Jesus. Jesus looking at him said, Thou art Simon, the son of Jonas; thou shalt be called Cephas (which interpreted is stone).
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 On the morrow he would go forth into Galilee, and Jesus finds Philip, and says to him, Follow me.
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 And Philip was from Bethsaida, of the city of Andrew and Peter.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Philip finds Nathanael, and says to him, We have found him of whom Moses wrote in the law, and the prophets, Jesus, the son of Joseph, who is from Nazareth.
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 And Nathanael said to him, Can anything good come out of Nazareth? Philip says to him, Come and see.
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Jesus saw Nathanael coming to him, and says of him, Behold [one] truly an Israelite, in whom there is no guile.
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Nathanael says to him, Whence knowest thou me? Jesus answered and said to him, Before that Philip called thee, when thou wast under the fig-tree, I saw thee.
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Nathanael answered and said to him, Rabbi, thou art the Son of God, thou art the King of Israel.
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 Jesus answered and said to him, Because I said to thee, I saw thee under the fig-tree, believest thou? Thou shalt see greater things than these.
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 And he says to him, Verily, verily, I say to you, Henceforth ye shall see the heaven opened, and the angels of God ascending and descending on the Son of man.
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”

< John 1 >