< Zechariah 13 >

1 In that day, there will be a fountain open to the house of David and to the inhabitants of Jerusalem, for the washing of the transgressor and of the defiled woman.
“A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
2 And this shall be in that day, says the Lord of hosts: I will disperse the names of the idols from the earth, and they will not be remembered any longer. And I will take away the false prophets and the unclean spirit from the earth.
“A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
3 And this shall be: when any devotee will continue to prophesy, his father and his mother, who conceived him, will say to him, “You shall not live, because you have been speaking a lie in the name of the Lord.” And his father and his mother, his own parents, will pierce him, when he will prophesy.
In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
4 And this shall be: In that day, the prophets will be confounded, each one by his own vision, when he will prophesy. Neither will they be covered with a garment of sackcloth in order to deceive.
“A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
5 But he will say, “I am not a prophet; I am a man of agriculture. For Adam has been my example from my youth.”
Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
6 And they will say to him, “What are these wounds in the middle of your hands?” And he will say, “I was wounded with these in the house of those who love me.”
In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
7 Awake, O spear, against my shepherd and against the man that clings to me, says the Lord of hosts. Strike the shepherd, and the sheep will be scattered. And I will turn my hand to the little ones.
“Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
8 And there will be in all the earth, says the Lord, two parts in it will be scattered and will pass away, and the third part will be left behind.
A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
9 And I will lead the third part through fire, and I will burn them just as silver is burned, and I will test them just as gold is tested. They will call on my name, and I will heed them. I will say, “You are my people.” And they will say, “The Lord is my God.”
Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”

< Zechariah 13 >