< Zechariah 12 >

1 The burden of the word of the Lord upon Israel. The Lord, stretching forth the heavens and founding the earth and forming the spirit of man within him, says:
Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
2 Behold, I will set Jerusalem as a lintel of the effects of drunkenness to all the surrounding peoples, yet even Judah will be in the blockade against Jerusalem.
“Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
3 And this shall be: In that day, I will set Jerusalem as a burdensome stone to every people. All who will lift it up will be torn to pieces. And all the kingdoms of the earth will be gathered together against her.
A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
4 In that day, says the Lord, I will strike every horse with stupor and his rider with madness. And I will open my eyes upon the house of Judah, and I will strike every horse of the people with blindness.
A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
5 And the governors of Judah will say in their heart, “Let the inhabitants of Jerusalem be strengthened for me, in the Lord of hosts, their God.”
Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
6 In that day, I will set the governors of Judah like a flaming furnace among wood, and like a flaming torch among hay. And they will devour, to the right and to the left, all the surrounding peoples. And Jerusalem will be inhabited again, in her own place, in Jerusalem.
“A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
7 And the Lord will save the tabernacles of Judah, just as in the beginning, so that the house of David and the glory of the inhabitants of Jerusalem may not glorify themselves boastfully against Judah.
“Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
8 In that day, the Lord will protect the inhabitants of Jerusalem, and even he who will have offended from them, in that day, will be like David, and the house of David will be like that of God, just like an angel of the Lord in their sight.
A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
9 And this shall be in that day: I will seek to crush all the Gentiles that come against Jerusalem.
A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
10 And I will pour out upon the house of David and upon the inhabitants of Jerusalem, the spirit of grace and of prayers. And they will look upon me, whom they have pierced, and they will mourn for him as one mourns for an only son, and they will feel sorrow over him, as one would be sorrowful at the death of a firstborn.
“Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
11 In that day, there will be a great lamentation in Jerusalem, like the lamentation of Hadadrimmon in the plain of Megiddo.
A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
12 And the earth will mourn: families and families separately; the families of the house of David separately, and their women separately;
Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
13 the families of the house of Nathan separately, and their women separately; the families of the house of Levi separately, and their women separately; the families of Shimei separately, and their women separately;
iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
14 all the rest of the families, families and families separately, and their women separately.
dukan sauran iyalan kuma da matansu.

< Zechariah 12 >