< Zechariah 11 >

1 Open your gates, Lebanon, and let fire consume your cedars.
Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
2 Howl, you fir tree, for the cedar has fallen, because the magnificent have been devastated. Howl, you oaks of Bashan, because the secure forest passage has been cut down.
Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
3 The voice of the howling of the shepherds: for their magnificence has been devastated. The voice of the roaring of the lions: because the arrogance of the Jordan has been devastated.
Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
4 Thus says the Lord my God: Feed the flock of the slaughter,
Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
5 which those who possessed them cut down, and they did not feel sorrow, and they sold them, saying: “Blessed be the Lord; we have become wealthy. Even their shepherds did not spare them.”
Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
6 And so, I will no longer spare the inhabitants upon the earth, says the Lord. Behold, I will deliver men, each one into the hand of his neighbor and into the hand of his king. And they will cut down the land, and I will not rescue it from their hand.
Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
7 And I will pasture the flock of the slaughter, because of this, O poor of the flock. And I took to myself two staffs: the one I called Handsome, and the other I called Rope, and I pastured the flock.
Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
8 And I cut down three shepherds in one month. And my soul became contracted concerning them, just as their soul also varied concerning me.
Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
9 And I said: I will not pasture you. Whatever dies, let it die. And whatever is cut down, let it be cut down. And let the rest of them devour, each one the flesh of his neighbor.
na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
10 And I took my staff, which was called Handsome, and I tore it apart, so as to invalidate my pact, which I had struck with all of the people.
Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
11 And it became invalid in that day. And so they understood, just like the poor of the flock who stay close to me, that this is the word of the Lord.
An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
12 And I said to them: If it is good in your eyes, bring me my wages. And if not, remain still. And they weighed for my wages thirty silver coins.
Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
13 And the Lord said to me: Cast it towards the statuary, the handsome price at which I have been valued by them. And I took the thirty silver coins, and I cast them into the house of the Lord, towards the statuary.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
14 And I cut short my second staff, which was called Rope, so that I might dissolve the brotherhood between Judah and Israel.
Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
15 And the Lord said to me: Still they are to you the equipment of a foolish shepherd.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
16 For behold, I will raise up a shepherd in the land, who will not visit what is forsaken, nor seek what is scattered, nor heal what is broken, nor nourish what remains standing, and he will consume the flesh of the fatted ones and break their hoofs.
Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
17 O shepherd and idol, abandoning the flock, with a sword upon his arm and over his right eye: his arm will be withered by drought, and his right eye will be obscured by darkness.
“Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”

< Zechariah 11 >