< Ruth 2 >

1 But there was a man related to Elimelech, a powerful man, and very wealthy, named Boaz.
To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
2 And Ruth, the Moabite, said to her mother-in-law, “If you order, I will go into the field and gather the ears of grain which escape the reaping hand, wherever I will find favor with the father of a family, who will be compassionate to me.” She answered her, “Go, my daughter.”
Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
3 And so she went and gathered the ears of grain after the completion of the reaping. But it happened that this field was owned by Boaz, who was of the kindred of Elimelech.
Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
4 And behold, he came out of Bethlehem and said to the reapers, “The Lord be with you.” They answered him, “May the Lord bless you.”
Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
5 And Boaz said to the young man who was in charge of the reapers, “Whose young woman is this?”
Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
6 He answered him, “This is the Moabite woman, who came with Naomi, from the land of the Moabites,
Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
7 and she asked to gather the remnants of the ears of grain, following the steps of the reapers, and from morning until now she has remained in the field, and, indeed, not for one moment has she returned home.”
Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
8 And Boaz said to Ruth, “Listen to me, daughter. Do not go to gather in any other field, nor depart from this place, but join with my young women,
Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
9 and follow where they reap. For I have given orders to my young men, so that no one is to harass you. And so, whenever you are thirsty, go to the vessels, and drink from the waters that the young men also drink.”
Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
10 She, falling on her face and paying homage on the ground, said to him: “How did this happen to me, that I should find favor before your eyes, and that you would condescend to accept me, a foreign woman?”
Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
11 He answered her, “Everything has been reported to me, what things you have done for your mother-in-law after the death of your husband, and how you left your parents, and the land in which you were born, and came to a people you did not know before.
Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
12 May the Lord repay you for your work, and may you receive a full reward from the Lord, the God of Israel, to whom you have come, and under whose wings you have taken refuge.”
Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
13 She said, “I have found favor before your eyes, my lord, who has consoled me, and you have spoken to the heart of your handmaid, who is unlike one of your young women.”
Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
14 And Boaz said to her, “When mealtime begins, come here, and eat bread, and dip your morsel in the vinegar.” And so she sat beside the reapers, and she piled up parched grain for herself, and she ate and was satisfied, and carried off the leftovers.
A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
15 And then she arose from there, so as to gather the ears of grain, according to the custom. But Boaz commanded his servants, saying, “If she is even willing to reap with you, do not prevent her,
Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
16 and purposely let fall some from your bundles, and allow them to remain, so that she may gather without blushing, and let no one rebuke her gathering.”
Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
17 And so she gathered in the field until evening. And striking and threshing with a staff what she had gathered, she found about the measure of an ephah of barley, that is, three measures.
Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
18 Carrying this, she returned into the city and showed it to her mother-in-law. Moreover, she offered it to her and even gave her the leftovers of her food, with which she had been satisfied.
Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
19 And her mother-in-law said to her, “Where have you gathered today, and where have you found work? Blessed is he who took pity on you!” And she informed her with whom she had been working, and she said the man’s name, that he was called Boaz.
Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
20 Naomi answered her, “May he be blessed by the Lord, because the same kindness which he provided for the living, he also kept for the dead.” And again she said: “This man is our near relative.”
Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
21 And Ruth said, “He charged me with this also, that from now on I should join with his reapers until all the crop has been reaped.”
Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
22 And her mother-in-law said to her, “It is better, my daughter, to go out reaping with his young women, lest in a stranger’s field someone may confront you.”
Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
23 And so, she joined with the young women of Boaz, and from then on reaped with them, until the barley and the wheat were stored in the barns.
Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.

< Ruth 2 >