< Psalms 80 >

1 Unto the end. For those who will be changed. The testimony of Asaph. A Psalm. The One who reigns over Israel: Be attentive. For you lead Joseph like a sheep. The One who sits upon the cherubim: Shine forth
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 in the presence of Ephraim, Benjamin, and Manasseh. Awaken your power and draw near, so as to accomplish our salvation.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Convert us, O God. And reveal your face, and we will be saved.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 O Lord, God of hosts, how long will you be angry over the prayer of your servant?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 How long will you feed us the bread of tears, and give us to drink a full measure of tears?
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 You have set us as a contradiction to our neighbors. And our enemies have ridiculed us.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 O God of hosts, convert us. And reveal your face, and we will be saved.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 You have transferred a vineyard from Egypt. You have cast out the Gentiles, and planted it.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 You were the leader of the journey in its sight. You planted its roots, and it filled the earth.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 Its shadow covered the hills, and its branches covered the cedars of God.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 It extended its new branches even to the sea, and its new seedlings even to the river.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 So then, why have you destroyed its walls, so that all those who pass by the way gather its grapes?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 The wild boar of the forest has trampled it, and a single wild beast has laid waste to it.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Turn back, O God of hosts. Look down from heaven, and see, and visit this vineyard;
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 and complete what your right hand has planted, and look upon the son of man, whom you have confirmed for yourself.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 Whatever has been set on fire and dug under will perish at the rebuke of your countenance.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Let your hand be over the man on your right, and over the son of man, whom you have confirmed for yourself.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 For we do not depart from you, and you will revive us. And we will invoke your name.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 O Lord, God of hosts, convert us. And reveal your face, and we will be saved.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Psalms 80 >