< Psalms 78 >

1 The understanding of Asaph. O my people, attend to my law. Incline your ears to the words of my mouth.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 I will open my mouth in parables. I will speak about concepts that are from the beginning.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 We have heard and known such great things, as our fathers have described to us.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 These things have not been hidden from their sons in any generation: declaring the praises of the Lord, and his virtues, and the wonders that he has done.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 And he has received testimony with Jacob, and he has set a law within Israel. Such great things, he has commanded our fathers, so as to make these things known to their sons,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 so that another generation might know them, and so that the sons, who will be born and who will grow up, shall describe them to their sons.
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 So then, may they put their hope in God, and may they not forget the works of God, and may they seek his commandments.
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 May they not become like their fathers, a perverse and exasperating generation: a generation that does not straighten their heart and whose spirit is not trustworthy with God.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 The sons of Ephraim, who bend and shoot the bow, have been turned back in the day of battle.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 They have not kept the covenant of God. And they were not willing to walk in his law.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 And they have been forgetful of his benefits, and of his miracle, which he revealed to them.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 He performed miracles in the sight of their fathers, in the land of Egypt, in the field of Tanis.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 He broke the sea and he led them through. And he stationed the waters, as if in a vessel.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 And he led them with a cloud by day, and with illumination by fire throughout the night.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 He broke through the rock in the wasteland, and he gave them to drink, as if from the great abyss.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 He brought forth water from the rock, and he conducted the waters, as if they were rivers.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 And yet, they continued to sin against him. In a waterless place, they provoked the Most High with resentment.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 And they tempted God in their hearts, by asking for food according to their desires.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 And they spoke badly about God. They said, “Would God be able to prepare a table in the desert?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 He struck the rock, and so waters flowed and the torrents flooded, but would even he be able to provide bread, or provide a table, for his people?”
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Therefore, the Lord heard, and he was dismayed, and a fire was kindled within Jacob, and an anger ascended into Israel.
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 For they neither put their trust in God, nor did they hope in his salvation.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 And he commanded the clouds from above, and he opened the doors of heaven.
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 And he rained down manna upon them to eat, and he gave them the bread of heaven.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Man ate the bread of Angels. He sent them provisions in abundance.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 He transferred the south wind from heaven, and, in his virtue, he brought in the Southwest wind.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 And he rained down flesh upon them, as if it were dust, and feathered birds, as if they were the sand of the sea.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 And they fell down in the midst of their camp, encircling their tabernacles.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 And they ate until they were greatly satisfied, and he brought to them according to their desires.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 They were not cheated out of what they wanted. Their food was still in their mouth,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 and then the wrath of God came upon them. And he slew the fat ones among them, and he impeded the elect of Israel.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 In all these things, they continued to sin, and they were not trustworthy with his miracles.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 And their days faded away into vanity, and their years with haste.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 When he slew them, then they sought him. And they returned, and they drew near to him in the early morning.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 And they were mindful that God is their helper and that the Most High God is their redeemer.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 And they chose him with their mouth, and then they lied to him with their tongue.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 For their heart was not upright with him, nor have they been living faithfully in his covenant.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Yet he is merciful, and he will pardon their sins. And he will not destroy them. And he has abundantly turned aside his own wrath. And he did not enflame his wrath entirely.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 And he remembered that they are flesh: with a spirit that goes forth and does not return.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 How often did they provoke him in the desert and stir him to wrath in a waterless place?
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 And they turned back and tempted God, and they exasperated the Holy One of Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 They did not remember his hand, in the day that he redeemed them from the hand of the one troubling them.
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Thus, he positioned his signs in Egypt and his wonders in the field of Tanis.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 And he turned their rivers into blood, along with their rain showers, so that they could not drink.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 He sent among them the common fly, and it devoured them, and the frog, and it scattered them.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 And he gave up their fruits to mold and their labors to the locust.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 And he slew their vineyards with hail and their mulberry trees with severe frost.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 And he delivered their cattle to the hail and their possessions to fire.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 And he sent the wrath of his indignation among them: indignation and wrath and tribulation, sent forth by evil angels.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 He made way for the path of his anger. He did not spare their souls from death. And he enclosed their beasts of burden in death.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 And he struck all the first-born in the land of Egypt: the first-fruits of all their labor in the tabernacles of Ham.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 And he took away his own people like sheep, and he led them through the wilderness like a flock.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 And he led them out in hope, and they did not fear. And the sea covered their enemies.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 And he led them to the mountain of his sanctification: the mountain that his right hand had acquired. And he cast out the Gentiles before their face. And he divided their land by lot to them, with a line of distribution.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 And he caused the tribes of Israel to dwell in their tabernacles.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Yet they tempted and aggravated God Most High, and they did not keep his testaments.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 And they turned themselves aside, and they did not serve the covenant. In the same manner as their fathers, they were turned backwards, like a crooked bow.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 They impelled him to anger on their hills, and they provoked him to rivalry with their graven images.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 God listened, and he spurned them, and he reduced Israel greatly, almost to nothing.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 And he rejected the tabernacle of Shiloh, his tabernacle where he had dwelt among men.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 And he delivered their virtue into captivity, and their beauty into the hands of the enemy.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 And he enclosed his people with the sword, and he spurned his inheritance.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Fire consumed their young men, and their virgins were not lamented.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Their priests fell by the sword, and their widows did not weep.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 And the Lord was awakened, as if out of sleep, and like a powerful man impaired by wine.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 And he struck his enemies on the back. He gave them over to everlasting disgrace.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 And he rejected the tabernacle of Joseph, and he did not choose the tribe of Ephraim.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 But he chose the tribe of Judah: mount Zion, which he loved.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 And he built up his sanctuary, like a single-horned beast, in the land that he founded for all ages.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 And he chose his servant David, and he took him from the flocks of the sheep: he received him from following the ewes with their young,
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 in order to pasture Jacob his servant and Israel his inheritance.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 And he fed them with the innocence of his heart. And he led them with the understanding of his hands.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Psalms 78 >