< Psalms 73 >

1 A Psalm of Asaph. How good is God to Israel, to those who are upright in heart.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But my feet were nearly moved; my steps had nearly slipped.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For I was zealous over the iniquitous, seeing the peacefulness of sinners.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For they have no respect for their death, nor do they have support in their wounds.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 They are not with the hardships of men, nor will they be scourged with men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore, arrogance has held on to them. They have been covered with their iniquity and impiety.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their iniquity has proceeded, as if from fat. They have parted from the affection of the heart.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They have thought and spoken wickedness. They have spoken iniquity in high places.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set their mouth against heaven, and their tongue has traversed the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore, my people will be converted here, and fullness of days will be found in them.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And they said, “How would God know?” and, “Isn’t there knowledge in high places?”
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold, these are sinners, and, abounding in this age, they have obtained riches.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 And I said: So then, it is without purpose that I have justified my heart and washed my hands among the innocent.
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 And I have been scourged all day long, and I have received my chastisement in the mornings.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I were to say that I would explain this: Behold, I would condemn this nation of your sons.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 I considered, so that I might know this. It is a hardship before me,
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 until I may enter into the Sanctuary of God, and understand it to its last part.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 So, because of deceitfulness, truly, you have placed it before them. While they were being lifted up, you were casting them down.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How have they been brought to desolation? They have suddenly failed. They have perished because of their iniquity.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As a dream is to those who awaken, O Lord, so will you reduce their image to nothing in your city.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For my heart has been inflamed, and my temperament has been changed.
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 And so, I have been reduced to nothing, and I did not know it.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 I have become like a beast of burden to you, and I am always with you.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 You have held my right hand. And in your will, you have conducted me, and with your glory, you have taken me up.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 For what is there for me in heaven? And what do I wish for on earth before you?
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 My body has failed, and my heart: O God of my heart, and God my portion, into eternity.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For behold, those who put themselves far from you will perish. You have perished all those who fornicate away from you.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But it is good for me to adhere to God, to put my hope in the Lord God, so that I may announce all your prophecies, at the gates of the daughter of Zion.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >