< Psalms 71 >

1 A Psalm of David. Of the sons of Jonadab and the former captives. In you, O Lord, I have hoped; do not let me be brought to ruin forever.
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Free me by your justice, and rescue me. Incline your ear to me, and save me.
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Be a God of protection and a place of strength for me, so that you may accomplish my salvation. For you are my firmament and my refuge.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Rescue me, O my God, from the hand of the sinner, and from the hand of the unjust and those who act against the law.
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 For you, O Lord, are my patience: my hope from my youth, O Lord.
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 In you, I have been confirmed from conception. From my mother’s womb, you are my protector. In you, I will sing forever.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 I have become to many as if I were a portent, but you are a strong helper.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 Let my mouth be filled with praise, so that I may sing your glory, your greatness all day long.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Do not cast me off in the time of old age. Do not abandon me when my strength will fail.
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 For my enemies have spoken against me. And those who watched for my soul have taken counsel as one,
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 saying: “God has abandoned him. Pursue and overtake him. For there is no one to rescue him.”
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 O God, do not be far from me. O my God, provide for my assistance.
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 May they be confounded, and may they fail, who drag down my soul. Let them be covered with confusion and shame, who seek evils for me.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 But I will always have hope. And I will add more to all your praise.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 My mouth will announce your justice, your salvation all day long. For I have not known letters.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 I will enter into the powers of the Lord. I will be mindful of your justice alone, O Lord.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 You have taught me from my youth, O God. And so I will declare your wonders continuously,
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 even in old age and with grey hairs. Do not abandon me, O God, while I announce your arm to every future generation: your power
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 and your justice, O God, even to the highest great things that you have done. O God, who is like you?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 How great is the tribulation that you have revealed to me: very great and evil. And so, turning back, you have brought me to life, and you have led me back again from the abyss of the earth.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 You have multiplied your magnificence. And so, turning back to me, you have consoled me.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 Therefore, I will confess your truth to you, with the instruments of the Psalter. O God, I will sing psalms to you with stringed instruments, O Holy One of Israel.
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 My lips will exult, when I sing to you, and also my soul, which you have redeemed.
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 And even my tongue will meditate on your justice all day long, when those who seek evils for me have been confounded and set in awe.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psalms 71 >