< Psalms 69 >

1 Unto the end. For those who will be changed: of David. Save me, O God, for the waters have entered, even to my soul.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 I have become stuck in a deep quagmire, and there is no firm footing. I have arrived at the height of the sea, and a tempest has overwhelmed me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 I have endured hardships, while crying out. My jaws have become hoarse; my eyes have failed. Meanwhile, I hope in my God.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Those who hate me without cause have been multiplied beyond the hairs of my head. My enemies, who persecuted me unjustly, have been strengthened. Then I was required to pay for what I did not take.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 O God, you know my foolishness, and my offenses have not been hidden from you.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Let those who wait for you, O Lord, the Lord of hosts, not be shamed in me. Let those who seek you, O God of Israel, not be confounded over me.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 For because of you, I have endured reproach; confusion has covered my face.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 I have become a stranger to my brothers and a sojourner to the sons of my mother.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 For zeal for your house has consumed me, and the reproaches of those who reproached you have fallen upon me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 And I covered my soul with fasting, and it has become a reproach to me.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 And I put on a haircloth as my garment, and I became a parable to them.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Those who sat at the gate spoke against me, and those who drank wine made me their song.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 But as for me, truly, my prayer is to you, O Lord. This time has pleased you well, O God. In the multitude of your mercy, in the truth of your salvation, hear me.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Rescue me from the quagmire, so that I may not become trapped. Free me from those who hate me and from deep waters.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Do not allow the tempest of water to submerge me, nor the deep to absorb me. And do not allow the well to close in on me.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Hear me, O Lord, for your mercy is kind. Look upon me, according to the fullness of your compassion.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 And do not turn your face away from your servant, for I am in trouble: heed me quickly.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Attend to my soul, and free it. Rescue me, because of my enemies.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 You know my reproach, and my confusion, and my reverence.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 All those who trouble me are in your sight; my heart has anticipated reproach and misery. And I sought for one who might grieve together with me, but there was no one, and for one who might console me, and I found no one.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 And they gave me gall for my food. And in my thirst, they gave me vinegar to drink.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Let their table be a snare before them, and a retribution, and a scandal.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Let their eyes be darkened, so that they may not see, and may their back always be crooked.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Pour out your indignation upon them, and may the fury of your anger take hold of them.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 May their dwelling place be deserted, and may there be no one who dwells in their tabernacles.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 For they persecuted whomever you struck. And they have added to the grief of my wounds.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Assign an iniquity upon their iniquity, and may they not enter into your justice.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Delete them from the Book of the Living, and let them not be written down with the just.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 I am poor and sorrowful, but your salvation, O God, has taken me up.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 I will praise the name of God with a canticle, and I will magnify him with praise.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 And it will please God more than a new calf producing horns and hoofs.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Let the poor see and rejoice. Seek God, and your soul will live.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 For the Lord has heard the poor, and he has not despised his prisoners.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Let the heavens and the earth praise him: the sea, and everything that crawls in it.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 For God will save Zion, and the cities of Judah will be built up. And they will dwell there, and they will acquire it by inheritance.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 And the offspring of his servants will possess it; and those who love his name will dwell in it.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalms 69 >