< Psalms 5 >

1 Unto the end. For her who pursues the inheritance. A Psalm of David. O Lord, listen closely to my words. Understand my outcry.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
2 Attend to the voice of my prayer, my King and my God.
Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
3 For to you, I will pray. In the morning, Lord, you will hear my voice.
Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
4 In the morning, I will stand before you, and I will see. For you are not a God who wills iniquity.
Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
5 And the malicious will not dwell close to you, nor will the unjust endure before your eyes.
Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
6 You hate all who work iniquity. You will destroy all who speak a lie. The bloody and deceitful man, the Lord will abominate.
Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
7 But I am in the multitude of your mercy. I will enter your house. I will show adoration toward your holy temple, in your fear.
Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
8 Lord, lead me in your justice. Because of my enemies, direct my way in your sight.
Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
9 For there is no truth in their mouth: their heart is vain.
Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
10 Their throat is an open sepulcher. They have acted deceitfully with their tongues. Judge them, O God. Let them fall by their own intentions: according to the multitude of their impiety, expel them. For they have provoked you, O Lord.
Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
11 But let all those who hope in you rejoice. They will exult in eternity, and you will dwell in them. And all those who love your name will glory in you.
Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
12 For you will bless the just. You have crowned us, O Lord, as if with a shield of your good will.
Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.

< Psalms 5 >