< Psalms 18 >

1 Unto the end. For David, the servant of the Lord, who spoke the words of this canticle to the Lord, in the day that the Lord delivered him from the hand of all his enemies and from the hand of Saul. And he said: I will love you, O Lord my strength.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 The Lord is my firmament, my refuge, and my liberator. My God is my helper, and I hope in him: my protector, and the horn of my salvation, and my support.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 Praising, I will call upon the Lord. And I will be saved from my enemies.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 The sorrows of death surrounded me, and the torrents of iniquity dismayed me.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 The sorrows of Hell encompassed me, and the snares of death intercepted me. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 In my tribulation, I called upon the Lord, and I cried out to my God. And he listened to my voice from his holy temple. And my cry in his presence entered into his ears.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 The earth was shaken, and it trembled. The foundations of the mountains were disturbed, and they were shaken, because he was angry with them.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 A smoke ascended by his wrath, and a fire flared up from his face: coals were kindled by it.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 He bent the heavens, and they descended. And darkness was under his feet.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 And he ascended upon the cherubim, and he flew: he flew upon the feathers of the winds.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 And he set darkness as his hiding place, with his tabernacle all around him: dark waters in the clouds of the air.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 At the brightness that was before his sight, the clouds crossed by, with hail and coals of fire.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 And the Lord thundered from heaven, and the Most High uttered his voice: hail and coals of fire.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 And he sent forth his arrows and scattered them. He multiplied lightnings, and he set them in disarray.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Then the fountains of waters appeared, and the foundations of the world were revealed, by your rebuke, O Lord, by the inspiration of the Spirit of your wrath.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 He sent from on high, and he accepted me. And he took me up, out of many waters.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 He rescued me from my strongest enemies, and from those who hated me. For they had been too strong for me.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 They intercepted me in the day of my affliction, and the Lord became my protector.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 And he led me out, into a wide place. He accomplished my salvation, because he willed me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 And the Lord will reward me according to my justice, and he will repay me according to the purity of my hands.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For I have preserved the ways of the Lord, and I have not behaved impiously before my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 For all his judgments are in my sight, and his justice, I have not pushed away from me.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 And I will be immaculate together with him, and I will keep myself from my iniquity.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 And the Lord will reward me according to my justice and according to the purity of my hands before his eyes.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 With the holy, you will be holy, and with the innocent, you will be innocent,
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 and with the elect, you will be elect, and with the perverse, you will be perverse.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For you will save the humble people, but you will bring down the eyes of the arrogant.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 For you illuminate my lamp, O Lord. My God, enlighten my darkness.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 For in you, I will be delivered from temptation; and with my God, I will climb over a wall.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 As for my God, his way is undefiled. The eloquence of the Lord has been examined by fire. He is the protector of all who hope in him.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 For who is God, except the Lord? And who is God, except our God?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 It is God who has wrapped me with virtue and made my way immaculate.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 It is he who has perfected my feet, like the feet of deer, and who stations me upon the heights.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 It is he who trains my hands for battle. And you have set my arms like a bow of brass.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 And you have given me the protection of your salvation. And your right hand sustains me. And your discipline has corrected me unto the end. And your discipline itself will teach me.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 You have expanded my footsteps under me, and my tracks have not been weakened.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 I will pursue my enemies and apprehend them. And I will not turn back until they have failed.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 I will break them, and they will not be able to stand. They will fall under my feet.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 And you have wrapped me with virtue for the battle. And those rising up against me, you have subdued under me.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 And you have given the back of my enemies to me, and you have destroyed those who hated me.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They cried out, but there was none to save them, to the Lord, but he did not heed them.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 And I will crush them into dust before the face of the wind, so that I will obliterate them like the mud in the streets.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 You will rescue me from the contradictions of the people. You will set me at the head of the Gentiles.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 A people I did not know has served me. As soon as their ears heard, they were obedient to me.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 The sons of foreigners have been deceitful to me, the sons of foreigners have grown weak with time, and they have wavered from their paths.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 The Lord lives, and blessed is my God, and may the God of my salvation be exalted:
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 O God, who vindicates me and who subdues the people under me, my liberator from my enraged enemies.
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 And you will exalt me above those who rise up against me. From the iniquitous man, you will rescue me.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 Because of this, O Lord, I will confess to you among the nations, and I will compose a psalm to your name:
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 magnifying the salvation of his king, and showing mercy to David, his Christ, and to his offspring, even for all time.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< Psalms 18 >