< Psalms 139 >

1 Unto the end. A Psalm of David. O Lord, you have examined me, and you have known me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 You have known my sitting down and my rising up again.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 You have understood my thoughts from afar. My path and my fate, you have investigated.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 And you have foreseen all my ways. For there is no word in my tongue.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Behold, O Lord, you have known all things: the newest and the very old. You have formed me, and you have placed your hand over me.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 Your knowledge has become a wonder to me. It has been reinforced, and I am not able to prevail against it.
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Where will I go from your Spirit? And where will I flee from your face?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 If I ascend into heaven, you are there. If I descend into Hell, you are near. (Sheol h7585)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
9 If I assume my feathers in early morning, and dwell in the utmost parts of the sea,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 even there, your hand will lead me forth, and your right hand will hold me.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 And I said: Perhaps darkness will overwhelm me, and the night will be my illumination, to my delight.
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 But darkness will not be impenetrable to you, and night will illuminate like the day: for just as its darkness is, so also is its light.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 For you have possessed my temperament. You have supported me from the womb of my mother.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 I will confess to you, for you have been magnified terribly. Your works are miraculous, as my soul knows exceedingly well.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 My bone, which you have made in secret, has not been hidden from you, and my substance is in accord with the lower parts of the earth.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Your eyes saw my imperfection, and all this shall be written in your book. Days will be formed, and no one shall be in them.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 But to me, O God, your friends have been greatly honored. Their first ruler has been exceedingly strengthened.
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 I will number them, and they will be more numerous than the sand. I rose up, and I am still with you.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 O God, if only you would cut down sinners. You men of blood: depart from me.
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 For you say in thought: They will accept your cities in vain.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Have I not hated those who hated you, Lord, and wasted away because of your enemies?
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 I have hated them with a perfect hatred, and they have become enemies to me.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Examine me, O God, and know my heart. Question me, and know my paths.
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 And see if there might be in me the way of iniquity, and lead me in the way of eternity.
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.

< Psalms 139 >