< Psalms 138 >

1 Of David himself. O Lord, I will confess to you with my whole heart, for you have heard the words of my mouth. I will sing psalms to you in the sight of the Angels.
Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
2 I will adore before your holy temple, and I will confess your name: it is above your mercy and your truth. For you have magnified your holy name above all.
Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
3 On whatever day that I will call upon you: hear me. You will multiply virtue in my soul.
Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
4 May all the kings of the earth confess to you, O Lord. For they have heard all the words of your mouth.
Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
5 And let them sing in accordance with the ways of the Lord. For great is the glory of the Lord.
Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
6 For the Lord is exalted, and he looks with favor on the humble. But the lofty he knows from a distance.
Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
7 If I wander into the midst of tribulation, you will revive me. For you extended your hand against the wrath of my enemies. And your right hand has accomplished my salvation.
Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
8 The Lord will provide retribution on my behalf. O Lord, your mercy is forever. Do not disdain the works of your hands.
Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.

< Psalms 138 >