< Psalms 12 >

1 Unto the end. For the octave. A Psalm of David. Save me, O Lord, because holiness has passed away, because truths have been diminished, before the sons of men.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 They have been speaking emptiness, each one to his neighbor; they have been speaking with deceitful lips and a duplicitous heart.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 May the Lord scatter all deceitful lips, along with the tongue that speaks malice.
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 They have said: “We will magnify our tongue; our lips belong to us. What is Lord to us?”
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 Because of the misery of the destitute and the groaning of the poor, now I will arise, says the Lord. I will place him in safety. I will act faithfully toward him.
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 The eloquence of the Lord is pure eloquence, silver tested by fire, purged from the earth, refined seven times.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 You, O Lord, will preserve us, and you will guard us from this generation into eternity.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 The impious wander aimlessly. According to your loftiness, you have multiplied the sons of men.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.

< Psalms 12 >