< Psalms 11 >

1 Unto the end. A Psalm of David. I trust in the Lord. How can you say to my soul, “Sojourn to the mountain, like a sparrow.”
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2 For behold, the sinners have bent their bow. They have prepared their arrows in the quiver, so as to shoot arrows in the dark at the upright of heart.
Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3 For they have destroyed the things that you have completed. But what has the just one done?
Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4 The Lord is in his holy temple. The Lord’s throne is in heaven. His eyes look upon the poor. His eyelids question the sons of men.
Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5 The Lord questions the just and the impious. Yet he who loves iniquity, hates his own soul.
Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6 He will rain down snares upon sinners. Fire and brimstone and windstorms will be the portion of their cup.
A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7 For the Lord is just, and he has chosen justice. His countenance has beheld equity.
Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.

< Psalms 11 >