< Psalms 108 >

1 A Canticle Psalm, of David himself. My heart is prepared, O God, my heart is prepared. I will sing songs, and I will sing psalms in my glory.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Rise up, my glory. Rise up, Psalter and harp. I will arise in early morning.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 I will confess to you, O Lord, among the peoples. And I will sing psalms to you among the nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 For your mercy is great, beyond the heavens, and your truth, even to the clouds.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Be exalted, O God, beyond the heavens, and your glory, beyond all the earth,
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 so that your beloved may be freed. Save with your right hand, and heed me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 God has spoken in his holiness. I will exult, and I will divide Shechem, and I will divide by measure the steep valley of tabernacles.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Gilead is mine, and Manasseh is mine, and Ephraim is the supporter of my head. Judah is my king.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab is the cooking pot of my hope. I will extend my shoe in Idumea; the foreigners have become my friends.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Who will lead me into the fortified city? Who will lead me, even into Idumea?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Will not you, O God, who had rejected us? And will not you, O God, go out with our armies?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Grant us help from tribulation, for vain is the help of man.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 In God, we will act virtuously, and he will bring our enemies to nothing.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.

< Psalms 108 >