< Psalms 107 >

1 Alleluia. Confess to the Lord, for he is good, for his mercy is with every generation.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let those who have been redeemed by the Lord say so: those whom he redeemed from the hand of the enemy and gathered from the regions,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 from the rising of the sun and its setting, from the north and from the sea.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 They wandered into solitude in a waterless place. They did not find the way of the city to be their dwelling place.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 They were hungry, and they were thirsty. Their soul fainted within them.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 And they cried out to the Lord in tribulation, and he rescued them in their necessity.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 And he led them in the right way, so that they might go forth to a city of habitation.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Let his mercies confess to the Lord, and let his miracles confess to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 For he has satisfied the empty soul, and he has satisfied the hungry soul with good things:
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 those sitting in darkness and in the shadow of death, shackled by extreme poverty and by iron.
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 For they exasperated the eloquence of God, and they irritated the deliberation of the Most High.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 And their heart was brought low with hardships. They were weakened, and there was no one to help them.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 And they cried out to the Lord in their tribulation, and he freed them from their distress.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 And he led them out of darkness and the shadow of death, and he broke apart their chains.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Let his mercies confess to the Lord, and let his miracles confess to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 For he has crushed the gates of brass and broken the iron bars.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 He has taken them up, from the way of their iniquity. For they were brought low, because of their injustices.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Their soul abhorred all food, and they drew near even to the gates of death.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 And they cried out to the Lord in their tribulation, and he delivered them in their necessity.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 He sent his word, and he healed them, and he rescued them from their utter destruction.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Let his mercies confess to the Lord, and let his miracles confess to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 And let them offer sacrifice with the sacrifice of praise, and let them announce his works in exultation.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Those who descend to the sea in ships, making their livelihood in the great waters:
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 these have seen the works of the Lord and his wonders in the deep.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 He spoke: and a windstorm stood up, and its waves were exalted.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 They ascend even to the heavens, and they descend even to the abyss. Their soul will waste away in distress.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 They were troubled, and they moved like a drunkard, and all their wisdom was consumed.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 And they cried out to the Lord in their tribulation, and he led them out of their distress.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 And he replaced the storm with a breeze, and its waves were stilled.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 And they were joyful that it was stilled, and he led them into the haven that they desired.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Let his mercies confess to the Lord, and let his miracles confess to the sons of men.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 And let them exalt him in the Church of the people, and praise him in the chair of the elders.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 He has placed rivers in the desert and sources of water in dry places,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 a fruit-bearing land in the midst of brine, before the malice of those who dwell in it.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 He has placed a desert in the midst of pools of waters, and a land without water in the midst of sources of water.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 And he has gathered the hungry together there, and they constructed a city of habitation.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 And they sowed fields and planted vineyards, and they produced the fruit of nativity.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 And he blessed them, and they were multiplied exceedingly. And he did not diminish their beasts of burden.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 And they became few, and they were afflicted by the tribulation of evils and of sorrow.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Contempt was poured over their leaders, and he caused them to wander in an impassable place, and not on the way.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 And he helped the poor out of destitution, and he stationed families like sheep.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 The upright will see, and they will rejoice. And every iniquity will block its mouth.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Who is wise and will keep these things? And who will understand the mercies of the Lord?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalms 107 >