< Numbers 25 >

1 Now Israel, at that time, dwelt in Shittim, and the people were fornicating with the daughters of Moab,
Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
2 who called them to their sacrifices. And they ate, and they adored their gods.
waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
3 And Israel was initiated into Baal of Peor. And so the Lord, being angry,
Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
4 said to Moses, “Take all the leaders of the people, and hang them on gallows against the sun, so that my fury may be averted from Israel.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
5 And Moses said to the judges of Israel, “Let each one kill his neighbors, who have been initiated into Baal of Peor.”
Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
6 And behold, one of the sons of Israel entered, in the sight of his brothers, to a prostitute of Midian, within view of Moses and of all the crowd of the sons of Israel, who were weeping before the door of the tabernacle.
Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
7 And when Phinehas the son of Eleazar, the son of Aaron the priest, had seen it, he rose up from the midst of the multitude, and, seizing a dagger,
Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
8 he entered after the Israelite man, into the brothel, and he pierced both of them at the same time, specifically, the man and the woman at the location of their genitals. And the scourge ceased from among the sons of Israel.
ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
9 And there were slain twenty-four thousand men.
Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
10 And the Lord said to Moses:
Ubangiji ya ce wa Musa,
11 “Phinehas the son of Eleazar, the son of Aaron the priest, has averted my wrath from the sons of Israel. For he was moved against them by my zeal, so that I myself, in my zeal, might not wipe away the sons of Israel.
“Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
12 Because of this, say to him: Behold, I give to him the peace of my covenant.
Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
13 And the covenant of the everlasting priesthood shall be as much for him as for his offspring. For he was zealous on behalf of his God, and he has made expiation for the wickedness of the sons of Israel.”
Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
14 Now the name of the Israelite man, who was killed with the Midianite woman, was Zimri the son of Salu, a leader from the kinship and tribe of Simeon.
Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
15 Moreover, the Midianite woman, who was put to death together with him, was called Cozbi the daughter of Zur, a most noble leader among the Midianites.
Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
16 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 “Let the Midianites perceive you as enemies, and strike them down,
“Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
18 for they, too, have behaved with hostility against you, and they have deceived you insidiously by means of the idol Peor, and by Cozbi, the daughter of a commander of Midian, their sister, who was struck down in the day of the scourge because of the sacrilege of Peor.”
gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”

< Numbers 25 >