< Numbers 26 >

1 After the blood of the guilty was shed, the Lord said to Moses, and to Eleazar the son of Aaron the priest:
Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
2 “Number the entire sum of the sons of Israel, from twenty years and above, by their houses and kinships, all who are able to go forth to war.”
“Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
3 And so, Moses and Eleazar the priest, who were in the plains of Moab, above the Jordan, opposite Jericho, spoke to those who were
Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
4 from twenty years and above, just as the Lord had commanded. And this is their number:
“Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
5 Ruben, the firstborn of Israel; his son, Hanoch, from whom is the family of the Hanochites; and Pallu, from whom is the family of the Palluites;
Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
6 and Hezron, from whom is the family of the Hezronites; and Carmi, from whom is the family of the Carmites.
daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
7 These are the families of the stock of Ruben, whose number was found to be forty-three thousand and seven hundred thirty.
Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
8 The son of Phallu: Eliab;
Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
9 his sons, Nemuel and Dathan and Abiram. These are Dathan and Abiram, the leaders of the people, who rose up against Moses and Aaron in the sedition at Korah, when they rebelled against the Lord.
’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
10 And the earth, opening its mouth, devoured Korah, with many others dying, when the fire burned two hundred fifty men. And a great miracle was wrought,
Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
11 so that, when Korah perished, his sons did not perish.
Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
12 The sons of Simeon, by their kinships: Nemuel, from him is the family of the Nemuelites; Jamin, from him is the family of the Jaminites; Jachin, from him is the family of the Jachinites;
Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
13 Sohar, from him is the family of the Soharites; Shaul, from him is the family of the Shaulites.
daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
14 These are the families of the stock of Simeon, whose entire number was twenty-two thousand two hundred.
Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
15 The sons of Gad, by their kinships: Zephon, from him is the family of the Zephonites; Haggi, from him is the family of the Haggites; Shuni, from him is the family of the Shunites;
Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
16 Ozni, from him is the family of the Oznites; Eri, from him is the family of the Erites;
daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
17 Arod, from him is the family of the Arodites; Areli, from him is the family of the Arelites.
daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
18 These are the families of Gad, whose entire number was forty thousand five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
19 The sons of Judah: Er and Onan, who both died in the land of Canaan.
Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
20 And these were the sons of Judah, by their kinships: Shelah, from whom is the family of the Shelahites; Perez, from whom is the family of the Perezites; Zerah, from whom is the family of the Zerahites.
Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
21 Moreover, the sons of Phares were: Hezron, from whom is the family of the Hezronites; and Hamul, from whom is the family of the Hamulites.
Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
22 These are the families of Judah, whose entire number was seventy-six thousand five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
23 The sons of Issachar, by their kinships: Tola from whom is the family of the Tolaites; Puvah, from whom is the family of the Puvahites;
Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
24 Jashub, from whom is the family of the Jashubites; Shimron, from whom is the family of the Shimronites.
daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
25 These are the kinships of Issachar, whose number was sixty-four thousand three hundred.
Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
26 The sons of Zebulon by their kinships: Sered, from whom is the family of the Seredites; Elon, from whom is the family of the Elonites; Jahleel, from whom is the family of the Jahleelites.
Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
27 These are the kinships of Zebulun, whose number was sixty thousand five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
28 The sons of Joseph by their kinships: Manasseh and Ephraim.
Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
29 From Manasseh was born Machir, from whom is the family of the Machirites. Machir conceived Gilead, from whom is the family of the Gileadites.
Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
30 Gilead had sons: Jezer, from whom is the family of the Jezerites; and Helek, from whom is the family of the Helekites;
Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
31 and Asriel, from whom is the family of the Asrielites; and Shechem, from whom is the family of the Shechemites;
daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
32 and Shemida, from whom is the family of the Shemidaites; and Hepher, from whom is the family of the Hepherites.
daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
33 Now Hepher was the father of Zelophehad, who had no sons, but only daughters, whose names are these: Mahlah, and Noa, and Hoglah, and Milcah, and Tirzah.
(Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
34 These are the families of Manasseh, and their number was fifty-two thousand seven hundred.
Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
35 Now the sons of Ephraim by their kinships were these: Shuthelah, from whom is the family of the Shuthelahites; Becher, from whom is the family of the Becherites; Tahan, from whom is the family of the Tahanites.
Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
36 Furthermore, the son of Shuthelah was Eran, from whom is the family of the Eranites.
Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
37 These are the kinships of the sons of Ephraim, whose number was thirty-two thousand five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
38 These are the sons of Joseph by their families: the sons of Benjamin in their kinships: Bela, from whom is the family of the Belaites; Ashbel, from whom is the family of the Ashbelites; Ahiram, from whom is the family of the Ahiramites;
Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
39 Shupham, from whom is the family of the Shuphamites; Hupham, from whom is the family of the Huphamites.
daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
40 The sons of Bela: Arad and Naaman. From Arad, the family of the Aradites; from Naaman, the family of the Naamanites.
Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
41 These are the sons of Benjamin by their kinships, whose number was forty-five thousand six hundred.
Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
42 The sons of Dan by their kinships: Shuham, from whom is the family of the Shuhamites. These are the kinships of Dan by their families.
Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
43 All these were Shuhamites, whose number was sixty-four thousand four hundred.
Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
44 The sons of Asher by their kinships: Imnah, from whom is the family of the Imnahites; Ishvi, from whom is the family of the Ishvites; Beriah, from whom is the family of the Beriahites.
Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
45 The sons of Beriah: Heber, from whom is the family of the Heberites; and Malchiel, from whom is the family of the Malchielites.
daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
46 Now the name of the daughter of Asher was Serah.
(Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
47 These are the kinships of the sons of Asher, and their number was fifty-three thousand four hundred.
Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
48 The sons of Naphtali by their kinships: Jahzeel, from whom is the family of the Jahzeelites; Guni, from whom is the family of the Gunites;
Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
49 Jezer, from whom is the family of the Jezerites; Shillem, from whom is the family of the Shillemites.
daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
50 These are the kinships of the sons of Naphtali by their families, whose number was forty-five thousand four hundred.
Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
51 This is the sum of the sons of Israel, who were counted: six hundred thousand and one thousand seven hundred thirty.
Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
52 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
53 “The land shall be divided to these, as their possessions, according to the number of their names.
“Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
54 To the greater number you shall give a greater portion, and to the lesser number, a lesser portion. To each one, just as they have now been counted, a possession shall be delivered.
Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
55 Yet only in so far as the land is divided by lot to a tribe and to families.
Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
56 Whatever the lot will happen to be, it shall be accepted, either by the greater, or by the lesser.
Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
57 Likewise, this is the number of the sons of Levi by their families: Gershon, from whom is the family of the Gershonites; Kohath, from whom is the family of the Kohathites; Merari, from whom is the family of the Merarites.
Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
58 These are the families of Levi: The family of Libni, the family of Hebroni, the family of Mahli, the family of Mushi, the family of Korah. Yet truly, Kohath conceived Amram,
Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
59 who had a wife, Jochebed, the daughter of Levi, who was born to him in Egypt. She bore, to her husband Amram: sons, Aaron and Moses, as well as their sister, Miriam.
sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
60 From Aaron were born Nadab and Abihu, and Eleazar and Ithamar.
Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
61 Of these, Nadab and Abihu died, when they had offered strange fire before the Lord.
Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
62 And these were all who were numbered: twenty-three thousand of the male gender, from one month and above. For they were not counted among the sons of Israel, neither was a possession given to them with the others.
Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
63 This is the number of the sons of Israel, who were enrolled by Moses and by Eleazar the priest, in the plains of Moab, above the Jordan, opposite Jericho.
Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
64 Among these, not one of them was numbered before, by Moses and Aaron in the desert of Sinai.
Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
65 For the Lord had foretold that all would die in the wilderness. And not one of them remained, except Caleb the son of Jephunneh, and Joshua the son of Nun.
Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.

< Numbers 26 >