< Nahum 2 >

1 He ascends, who would scatter before your eyes, who would maintain the blockade. Contemplate the way, fortify your back, reinforce virtue greatly.
Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
2 For the Lord has repaid the arrogance of Jacob, just like the arrogance of Israel. For the despoilers have scattered them, and they have corrupted their procreation.
Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
3 The shield of his strong ones is fire, the men of war are in scarlet. The reins of the chariot are fiery in the day of his preparation, and the drivers have been drugged.
Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
4 They have become confused on their journey. The four-horse chariots have collided in the streets. Their appearance is like torches, like lightning dashing around.
Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
5 He will call to mind his strong ones; they will destroy along their journey. They will quickly ascend its walls, and a shelter will be prepared.
Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
6 The gates of the rivers have been opened, and the temple has been pulled down to the ground.
An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
7 And the foot soldier has been led away captive, and her handmaids were driven away, mourning like doves, murmuring in their hearts.
An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
8 And Nineveh, her waters are like a fish pond. Yet truly, they have fled away: “Stand, stand!” But there is no one who will turn back.
Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
9 Despoil the silver, despoil the gold. And there is no end to all the riches of desirable equipment.
A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
10 She has been scattered, and cut, and torn apart. And the heart melts, and the knees buckle, and weakness is in every temperament. And the faces of them all are like a black kettle.
Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
11 Where is the dwelling place of the lions, and the feeding ground of the young lions, to which the lion went, so as to open a way for the young lion, and so that there would be none to make them afraid?
Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
12 The lion seized enough for his young, and killed enough for his lionesses, and he filled his caves with prey, and his den with spoils.
Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
13 Behold, I will come to you, says the Lord of hosts, and I will burn your chariots even to smoke, and the sword will devour your young lions. And I will exterminate your prey from the land, and the voice of your messengers shall no longer be heard.
“Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”

< Nahum 2 >