< Micah 3 >

1 And I said: Listen, leaders of Jacob and chiefs of the house of Israel. Does it not belong to you to know judgment,
Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
2 you who hold hatred for good, and love evil, who violently steal their skins from over them and their flesh from over their bones?
ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
3 They have devoured the flesh of my people, and have stripped their skin from over them, and they have shattered and chopped their bones, as if for the kettle, and like flesh in the middle of the pot.
ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
4 Then they will cry out to the Lord, and he will not heed them. And he will hide his face from them in that time, just as they have acted wickedly with their inventions.
Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
5 Thus says the Lord about the prophets who seduce my people: They bite with their teeth and preach peace, and if anyone does not give something to their mouth, they sanctify a battle against him.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
6 Because of this, night will be yours for vision, and darkness yours for divination, and the sun will meet with death over the prophets, and the day will be darkened over them.
Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
7 And those who see visions will be confounded, and the diviners will be confounded. And they will all cover their faces, because there is no response from God.
Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
8 Nevertheless, truly I have been filled with the strength of the Spirit of the Lord, with judgment and virtue, in order to announce to Jacob his wickedness and to Israel his sin.
Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
9 Hear this, leaders of the house of Jacob and judges of the house of Israel, you who abominate judgment and who pervert all that is right.
Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
10 You build up Zion with blood, and Jerusalem with iniquity.
kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
11 Her leaders have judged for tributes, and her priests have taught for payment, and her prophets divined for money. And they leaned upon the Lord, saying: “Is not the Lord in our midst? No disaster will overcome us.”
Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
12 For this reason, because of you, Zion will be plowed under like a field, and Jerusalem will become like a pile of stones, and the mountain of the temple like the high places of the forests.
Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.

< Micah 3 >