< Jonah 1 >

1 And the word of the Lord came to Jonah the son of Amittai, saying:
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 Rise and go to Nineveh, the great city, and preach in it. For its malice has ascended before my eyes.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 And Jonah rose in order to flee from the face of the Lord to Tarshish. And he went down to Joppa and found a ship bound for Tarshish. And he paid its fare, and he went down into it, in order to go with them to Tarshish from the face of the Lord.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 But the Lord sent a great wind into the sea. And a great tempest took place in the sea, and the ship was in danger of being crushed.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 And the mariners were afraid, and the men cried out to their god. And they threw the containers that were in the ship into the sea in order to lighten it of them. And Jonah went down into the interior of the ship, and he fell into a painful deep sleep.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 And the helmsman approached him, and he said to him, “Why are you weighed down with sleep? Rise, call upon your God, so perhaps God will be mindful of us and we might not perish.”
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 And a man said to his shipmate, “Come, and let us cast lots, so that we may know why this disaster is upon us.” And they cast lots, and the lot fell upon Jonah.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 And they said to him: “Explain to us what is the reason that this disaster is upon us. What is your work? Which is your country? And where are you going? Or which people are you from?”
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 And he said to them, “I am Hebrew, and I fear the Lord God of heaven, who made the sea and the dry land.”
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 And the men were greatly afraid, and they said to him, “Why have you done this?” (For the men knew that he was fleeing from the face of the Lord, because he had told them.)
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 And they said to him, “What are we to do with you, so that the sea will cease for us?” For the sea flowed and swelled.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 And he said to them, “Take me, and cast me into the sea, and the sea will cease for you. For I know that it is because of me that this great tempest has come upon you.”
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 And the men were rowing, so as to return to dry land, but they did not succeed. For the sea flowed and swelled against them.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 And they cried out to the Lord, and they said, “We beseech you, Lord, do not let us perish for this man’s life, and do not attribute to us innocent blood. For you, Lord, have done just as it pleased you.”
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 And they took Jonah and cast him into the sea. And the sea was stilled from its fury.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 And the men feared the Lord greatly, and they sacrificed victims to the Lord, and they made vows.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 And the Lord prepared a great fish to swallow Jonah. And Jonah was in the belly of the fish for three days and three nights.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.

< Jonah 1 >