< Leviticus 18 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to the sons of Israel, and you shall say to them: I am the Lord your God.
“Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
3 You shall not act according to the custom of the land of Egypt, in which you have lived; nor shall you behave according to the habit of the region of Canaan, into which I will lead you; neither shall you walk in their ordinances.
Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
4 You shall accomplish my judgments, and you shall observe my precepts, and you shall walk in them. I am the Lord your God.
Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 Keep my laws and judgments; when a man does these, he shall live by them. I am the Lord.
Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
6 No man shall approach her who is a close blood-relative to him, so as to uncover her nakedness. I am the Lord.
“‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
7 You shall not expose the nakedness of your father, or the nakedness of your mother. She is your mother; you shall not uncover her nakedness.
“‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
8 You shall not expose the nakedness of your father’s wife; for it is the nakedness of your father.
“‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
9 You shall not uncover the nakedness of your sister, whether from father or from mother, whether she was born at home or abroad.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
10 You shall not uncover the nakedness of your son’s daughter, or your daughter’s daughter; for it is your own nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
11 You shall not uncover the nakedness of your father’s wife’s daughter, whom she bore to your father, and who is your sister.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
12 You shall not expose the nakedness of your father’s sister; for she is the flesh of your father.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
13 You shall not uncover the nakedness of your mother’s sister, because she is the flesh of your mother.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
14 You shall not uncover the nakedness of your father’s brother, nor shall you approach his wife, who is joined to you by affinity.
“‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
15 You shall not uncover the nakedness of your daughter-in-law, for she is your son’s wife; neither shall you expose her dishonor.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
16 You shall not uncover the nakedness of your brother’s wife; for it is the nakedness of your brother.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
17 You shall not uncover the nakedness of your wife and her daughter. You shall not take her son’s daughter or her daughter’s daughter, so as to uncover her dishonor; for they are her flesh, and such sexual intercourse is incest.
“‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
18 You shall not take your wife’s sister as a rival mistress; nor shall you uncover her nakedness, while your wife is still living.
“‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
19 You shall not approach a woman who is undergoing menstruation, nor shall you uncover her foulness.
“‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
20 You shall not have sexual intercourse with your neighbor’s wife, nor shall you be defiled by the mingling of seed.
“‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
21 You shall not give some of your seed to be consecrated to the idol Moloch, nor to pollute the name of your God. I am the Lord.
“‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
22 You shall not commit sexual acts with a male, in place of sexual intercourse with a female, for this is an abomination.
“‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
23 You shall not commit sexual acts with any animal, nor shall you be defiled by it. A woman shall not lie down with a beast, nor commit sexual acts with it; for this is wickedness.
“‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
24 Do not pollute yourselves with any of these things, by which all of the nations, which I will cast out in your sight, have been contaminated
“‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
25 and by which the land has been polluted. I will visit the wickedness of the land, so that it may vomit out its inhabitants.
Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
26 Keep my ordinances and judgments, and do not do any of these abominations: the native born, as well as the settler, who sojourns among you.
Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
27 For all these detestable things were done by the inhabitants of the land who were here before you, and they have polluted it.
gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
28 Therefore, beware, lest in a similar manner, it may vomit you out as well, if you do these same things, just as it vomited out the people who were before you.
Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
29 Every soul who shall commit any of these abominations shall perish from the midst of his people.
“‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
30 Keep my commandments. Do not be willing to do the things which have been done by those who were before you, and do not be polluted by these things. I am the Lord your God.
Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Leviticus 18 >