< Judges 4 >

1 But after the death of Ehud, the sons of Israel resumed doing evil in the sight of the Lord.
Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
2 And the Lord delivered them into the hands of Jabin, the king of Canaan, who reigned at Hazor. And he had a commander of his army named Sisera, but this man lived at Harosheth of the Gentiles.
Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
3 And the sons of Israel cried out to the Lord. For he had nine hundred chariots with scythes, and he vehemently oppressed them for twenty years.
Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
4 Now there was a prophetess, Deborah, the wife of Lappidoth, who judged the people in that time.
A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
5 And she was sitting under a palm tree, which was called by her name, between Ramah and Bethel, on Mount Ephraim. And the sons of Israel went up to her for every judgment.
Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
6 And she sent and called Barak, the son of Abinoam, from Kedesh of Naphtali. And she said to him: “The Lord, the God of Israel, instructs you: ‘Go and lead an army to Mount Tabor, and you shall take with you ten thousand fighting men from the sons of Naphtali and from the sons of Zebulun.
Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
7 Then I will lead to you, at the place of the torrent Kishon, Sisera, the leader of the army of Jabin, with his chariots and the entire multitude. And I will deliver them into your hand.’”
Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
8 And Barak said to her: “If you will come with me, I will go. If you are not willing to come with me, I will not go.”
Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
9 She said to him: “Indeed, I will go with you. But due to this change, the victory shall not be reputed to you. And so Sisera will be delivered into the hand of a woman.” Therefore, Deborah rose up, and she traveled with Barak to Kedesh.
Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
10 And he, summoning Zebulun and Naphtali, ascended with ten thousand fighting men, having Deborah in his company.
a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
11 Now Heber, the Kenite, had previously withdrawn from the rest of the Kenites, his brothers, the sons of Hobab, the relative of Moses. And he had pitched his tents as far as the valley that is called Zaanannim, which was near Kedesh.
To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
12 And it was reported to Sisera that Barak, the son of Abinoam, had ascended to Mount Tabor.
Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
13 And he gathered together the nine hundred chariots with scythes, and the entire army, from Harosheth of the Gentiles to the torrent Kishon.
sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
14 And Deborah said to Barak: “Rise up. For this is the day on which the Lord delivers Sisera into your hands. For he is your commander.” And so, Barak descended from Mount Tabor, and the ten thousand fighting men with him.
Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
15 And the Lord struck Sisera with great fear, and all his chariots and all his multitude with the edge of the sword, in the sight of Barak, so much so that Sisera, leaping from his chariot, fled on foot.
Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
16 And Barak pursued the fleeing chariots, and the army, as far as Harosheth of the Gentiles. And the entire multitude of the enemy was cut down, unto utter annihilation.
Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
17 But Sisera, while fleeing, arrived at the tent of Jael, the wife of Heber, the Kenite. For there was peace between Jabin, the king of Hazor, and the house of Heber, the Kenite.
Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
18 Therefore, Jael went out to meet Sisera, and she said to him: “Enter to me, my lord. Enter, you should not be afraid.” And he entered her tent, and having been covered by her with a cloak,
Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
19 he said to her: “Give me, I beg you, a little water. For I am very thirsty.” And she opened a bottle of milk, and she gave him to drink. And she covered him.
Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
20 And Sisera said to her: “Stand before the door of the tent. And if anyone arrives, questioning you and saying, ‘Could there be any man here?’ you shall respond, ‘There is no one.’”
Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
21 And so Jael, the wife of Heber, took a spike from the tent, and also took a mallet. And entering unseen and with silence, she placed the spike over the temple of his head. And striking it with the mallet, she drove it through his brain, as far as the ground. And so, joining deep sleep to death, he fell unconscious and died.
Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
22 And behold, Barak arrived, in pursuit of Sisera. And Jael, going out to meet him, said to him, “Come, and I will show you the man whom you are seeking.” And when he had entered her tent, he saw Sisera lying dead, with the spike fixed in his temples.
Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
23 Thus did God humble Jabin, the king of Canaan, on that day, before the sons of Israel.
A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
24 And they increased every day. And with a strong hand they overpowered Jabin, the king of Canaan, until they wiped him out.
Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.

< Judges 4 >